• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tallafin Man Da Nijeriya Ke Biya Yanzu Ya Zarce Nb700 Duk Wata – IPMAN

by Khalid Idris Doya
11 months ago
in Labarai
0
Tallafin Man Da Nijeriya Ke Biya Yanzu Ya Zarce Nb700 Duk Wata – IPMAN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar ‘yan kasuwan mai masu zaman kanta (IPMAN), ta ce tallafin da ake kashewa a Nijeriya a bangaren mai ya zarce biliyan 700 duk wata.

  • Za A Ci Gaba Da Fuskantar Karancin Man Fetur – IPMAN
  • IPMAN Ta Yi Barazanar Rufe Gidajen Mai Sama Da 30,000 Saboda Bashi

Sakataren IPMAN, reshen Abuja-Suleja, Mohammed Shuaibu, shi ne ya shaida hakan a wata sanarwar manema labarai da ya fitar a ranar Litinin.

Yana maida martani ne kan bayanan da kungiyar ‘yan kasuwan makamashi a Nijeriya (MEMAN) suka fitar a ranar Laraba, ya lura kan cewa kudin saukar man fetur lita guda a wannan ranar ya kai naira 1,117.

Da yake magana kan bayanan kungiyar MEMAN, Shuaibu ya ce, da yiyuwar gwamnatin tarayya da kamfanin mai fetur na kasa ba za su fito su fadi gaskiya kan tallafin mai da kasar ke kashewa ba.

Sai ya gargadi ‘yan Nijeriya da cewa su fara zaman shirin fuskantar karin kudin mai fetur.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

“Farashin mai fetur na dogara ne kan karfin yawan bukatarsa da kuma yanayin wadatuwarsa a kasuwannin duniya. Duk lokacin da farashin ya karu a kasuwannin duniya, dole a Nijeriya ma ya shafemu.

“Don haka mu zauna da shirin fuskantar karin farashin mai a kowani lokaci, ka da mu sha mamaki domin tuni sun fada mana,” Shuaibu ya shaida.

Sai dai kuma, a wurare daban-daban, karamin ministan albarkatun mai fetur, Heineken Lokpobiri, ya sha nanata cewa an jima da cire tallafin man fetur a Nijeriya.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da aka fara samun takun tsaka tsakanin matatar man kamfanin Dangote da hukumar kula da samar da mai ta kasa kan batun ingancin albarkatun mai.

Idan za a tuna dai, a kwanakin baya tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir el-Rufai, ya yi ikirarin cewa gwamnatin Bola Tinibu tana biyan tallafin mai fiye ma abun da ake biya a baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IPMAN
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Baro Shiri Tun Rani Game Da Shigo Da Abinci Ba Tare Da Biyan Haraji Ba

Next Post

An Shiga Rudani Saboda Rashin Isar Tirelolin Shinkafar Tallafi Wasu Jihohi

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

43 minutes ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

4 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

4 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

14 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

16 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

17 hours ago
Next Post
An Shiga Rudani Saboda Rashin Isar Tirelolin Shinkafar Tallafi Wasu Jihohi

An Shiga Rudani Saboda Rashin Isar Tirelolin Shinkafar Tallafi Wasu Jihohi

LABARAI MASU NASABA

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.