• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taransifoma Ta Yi Ajalin Mutane 7 A Filato

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Filato

Al’ummar unguwar Kabong da ke Gada Biyu a karamar hukumar Jos ta Arewa a jihar Filato sun wayi gari da wani mummunar ibtila’in annoba da sanyin safiyar ranar Asabar biyo bayan bindiga da Taransifoma ta yi cikin dare da ta yi ajalin rayukan mutum 7 hadi da jikkata wasu da dama.

Wakilinmu ya labarto cewa wutar da ta tashi ta samu asali ne daga jikin na’urar rarraba wutar lantarki (taransifoma), inda mummunar gobara ta barke da ta janyo firgici da razani ga al’ummar unguwar.

  • Jerin ‘Yan Nijeriya Da Suka Shiga Sahun Fitattun Musulmi 500 A Duniya
  • Yadda Uwargida Za Ta Gyara Fuska Da Abubuwa Masu Sauki

A cewar ganau, wanda ya nemi kada a bayyana sunansa a jarida, ya ce, mutum bakwai ne suka mutu, kuma gidaje da shaguna da dama hade da kadarorin miliyoyin naira ne suka salwanta sakamakon tashin gobarar da ta samo asali daga fashewar taransifomar.

“Abun bakin ciki da takaici, biyu daga cikin mutanen da suka mutu din ‘yan gida daya ne, wanda hakan ya janyo bakin ciki da bacin rai ga ‘yan uwansu,” ya kara da cewa.

Kazalika, kamfanin rarraba wutar lantarki ta Jos (JED) ta tofa albarkacin bakinta kan annobar, inda ta ce ta kadu sosai bisa lamarin da ya faru tsakar daren ranar Asabar wanda ya shafi kwastominsu da ke amfani da na’urar rarraba wutar lantarki ta Kabong Primary a unguwar Kabong da ke kan hanyar Rububa a Jos, babban birnin jihar Filato.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

A sanarwar da shugaban sashin yada labarai na kamfanin, Dr. Friday Adakole Elijah, ya ce, binciken farko-farko da aka yi ya nuna cewa babban layin wuta mai dauke da balbalin wuta shi ne ya shiga layin karamin layukan wuta inda hakan ya janyo wutar ta tsallake iyakar da aka ware mata.

Ya ce, dukkanin matakan da ya dace su bi wajen tabbatar da gano hakikanin abun da ya janyo tashin wutar za su yi, kuma sun dauki matakan gaggawa na kare faruwar hakan a nan gaba.

Daga bisani kamfanin JED ya mika ta’aziyyarsa da jajantawarsa ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu da wadanda dukiyarsu ya salwanta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 
Labarai

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

October 15, 2025
sallah
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025
Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba
Labarai

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

October 15, 2025
Next Post
Mahaifiyar Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan Ta Rasu

Mahaifiyar Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan Ta Rasu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

October 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025
An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

October 15, 2025
sallah

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025
Mujallar “Qiushi” Za Ta Wallafa Muhimmiyar Kasidar Shugaba Xi Jinping Kan Muhimman Shawarwari Hudu Da Ya Gabatar

Mujallar “Qiushi” Za Ta Wallafa Muhimmiyar Kasidar Shugaba Xi Jinping Kan Muhimman Shawarwari Hudu Da Ya Gabatar

October 15, 2025
Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

October 15, 2025
Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

Xi Jinping Ya Taya Patrick Herminie Murnar Lashe Zaben Shugaban Kasar Seychelles

October 15, 2025
Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

October 15, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.