• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

by Idris Aliyu Daudawa
14 hours ago
in Labarai
0
Bello
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An haifi  Ahmadu Bello a garin Raba ranar   12 ga Yuni 1910. Mahaifinsa, Ibrahim Atiku Bello, shi ne Hakimin kuma ya riƙe muƙamin sarautar  Sarkin Rabah. Yana kuma daga tsatson mujaddadi Shehu Usman Danfodiyo wanda shi ne asalin masarautar Sakkwato,  babban jika ga Sarkin Musulmi Muhammadu Bello, kuma jikan Sarkin Musulmi Atiku na Rab.

Ya samu ilimin addinin musulunci tun a gidansu,inda ya koyi Karatun Alkur’ani da kuma Hadisan Manzon Allah Muhammad Sallallahu Alaihis Wasallam. Daganan kuma ya yi makarantar Sakkwato Midil Sukul, da kuma Kwalejin horar da Malamai ta Katsina (wadda yanzu ake kira da suna Kwalejin Barewa). Lokacin da yake ɗan makaranta ana kiransa da  Ahmadu Rabah. Sai dai wasu suna kiransa da Gamji. Ya kammala makarantar a shekarar 1931 daga bisani kuma ya zama Malamin makaranta mai koyar da Turanci a Midil Sukul ta Sakkwato.

  • Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
  • An Gano Karin Gawarwaki 3 Da Jirgin Ruwa Ya Kife Da Fasinjoji 26 A Sokoto

A shekarar 1934 ce aka naɗa, Ahmadu Bello matsayin Hakimin Raba wanda a lokacin Sarkin Musulmi Hassan Dan Mu’azu ya naɗa shi, inda ya gaji ɗanuwansa. A shekarar 1938 kuma sai aka ƙara masa girma,inda ya zama Hakimin Gusau (wato garin da ya zama babban birnin Jihar Zamfara) ya kuma zama ɗan majalisar Sarkin Musulmi a duk shekarar yana da shekara 28. A shekarar 1938, ya yi ƙoƙarin ya zama Sarkin Musulmi  wato Sultan amma bai samu sa’ar cimma burin nasa ba, sai Sarkin Musulmi Siddiƙ Abubakar 111, ya samu sarautar wadda sai da ya yi shekara 50, ya rasu ne a shekarar 1988.

Ba tare da ɓata lokaci ba sai sabon Sarkin Musulmin ya naɗa Ahmadu Bello ya bashi Sarautar Sardauna (wadda sarautar Yarima ce) na Sakkwato, sarauta ce ta gargajiya , ya ƙara ma shi girma ya maida shi majalisar ko majalisar gargajiya ta Sakkwato. Waɗannan muƙaman su sauka ba shi dama ta kasancewa mai ba Sarkin Musulmi shawara kan harkokin siyasa.Daga nan kuma  a ba shi muƙamain mai kulawa da Lardin Sakkwato domin ya riƙa kula da Hakimai  47, a shekrar 1944, sai aka sake maido shi fadar ta Sarkin Musulmi a matsayin babban Sakatare na mulkin masarautun gargajiya.

A shekarar 1940 sai ya shiga  Jam’iyyar Mutanen Arewa wadda a ƙarshe ta rikiɗe ta koma Northern People’s Congress (NPC) a shekarar 1951.Amma a shekarar 1948, ya tafi ƙasar Ingila akan tallafin karatu na gwamnati domin ya yi karatu kan lamarin daya shafi ƙananan Hukumomi ta haka ya ƙara koyon yadda ake tafiyar da mulki a gwamnatance.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BelloSardaunaTarihi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

Next Post

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Related

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta
Labarai

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

9 hours ago
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

12 hours ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

12 hours ago
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

15 hours ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

16 hours ago
Bello
Labarai

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

19 hours ago
Next Post
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken "Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani"

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

September 19, 2025
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaɗuwa Tsakanin Ma’aurauta

September 19, 2025
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

September 19, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Mahawara Na MDD Karo Na 80

September 19, 2025
Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Bello

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.