• English
  • Business News
Saturday, October 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Hassan Usman Katsina (1)

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 seconds ago
Hassan Usman Katsina

An haifi Hassan Usman Katsina ne a ranar 31, ga watan Maris shekarar 1933. Da ne ga mahaifinsa Sarkin Katsina Sir Usman Nagogo tare da abokin haihuwarsa Hussaini da ake kiransa da sunan (Naini). Sunan mahaifiyarsu Fatima, sai dai an fi kiran ta da sunan Cima ko Hajiya Uwargida ‘yar Wazirin Katsina, Haruna ce.

 

Hassan Usman Katsina bai kai shekara shida ba lokacin da aka kai shi gidan Kankiya Nuhu wanda shi Kaka ne a wurinsa domin kuwa kanen Sarkin Katsina Muhammdu Dikko. Kamar dai yadda aka saba a kasar Hausa lokacin da ayake tasowa ne aka kai shi makarantar Islamiyya ya yi karatun Allo. Daga shekarar 1940- 1944 ya yi makarantar Elemantare ta Kankiya daga can kuma sai ya wuce zuwa, makarantar Midil ta Katsina daga 1944-1947. Bugu da kari Hassan Usman Katsina ya halarci Kwalejin Barewa ta Zariya, daga 1948-1951.Daganan kuma sai makarantar koyon harkokin mulki ta Zariya a 1952, daganan kuma sai ya halarci Kwalejin Kimiyya da fasaha ta Njeriya da ke Zariya a 1953-1955.

  • Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
  • Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi

Kamar yadda abin ya kasance sai Hassan ya bada labarin “Watarana na zo wucewa zuwa wurin cin abinci sai na ga an manna takarda ta neman ‘yan Arewa wadanda suke sha’awar zuwa aikin soja. Sai na ce ina so; ni dai kawai na ji ina so ba da wani na yi shawara ba, na yi kokarin bin ka’idar shigar ne. Amma ban fada ba, don ba na son tsohuwata ta ji. Idan ta ji ba za ta yarda ba. Da aka yi hutu na koma gida sai na sanarwa mahaifina Sarkin Katsina Usman Nagogo, cewa ina sa ran takarda ta neman tafiyar makarantar horar da hafsoshin soja. Sai ya ce, ka fada wa Hajiya?’ Na ce ‘a’a ban fada mata ba’, Sai ya ce to kar ka fada mata”.

 

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique

Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia

Ya ci gaba da bayanin cewa, “Da zan koma Kaduna sai ya ba ni takarda na kai wa Wazirin Katsina, Alhaji Isa Kaita. Na zo Kaduna na yi jarrabawa, bayan mun kare na koma gida ina sauraren sakamakon jarrabawar. Ba zan taba mantawa ba, ana zaune wajen Hawan Daba don tarbar Sarauniyar Ingila sai na sami telegiram mai cewa na ci jarrabawa ana nema na a Kaduna.

 

“Na fadawa mahaifina. Muka kintsa muka bar Katsina sai Kaduna, daga Kaduna muka tafi Legas. Da isa ta Legas sai na ga abokan nawa da suka sami nasarar wannan tafiyar duk ‘yan Kudu ne. Ni kadai ne dan Arewa kuma Bahaushe cikin daga cikin mu takwas

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique

October 11, 2025
Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia
Daga Birnin Sin

Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia

October 11, 2025
Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa

October 11, 2025

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Hassan Usman Katsina (1)

Tarihin Hassan Usman Katsina (1)

October 11, 2025
An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique

An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique

October 11, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa

Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa

October 11, 2025
Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari

Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari

October 11, 2025
Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia

Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia

October 11, 2025
Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa

Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi

Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi

October 11, 2025
Gwamna Aliyu Ya Tsige Hakimai 15 Na Sokoto

A Ba Mu Makamai Don Kare Kanmu – Jama’ar Sakkwato

October 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.