• English
  • Business News
Thursday, May 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (1)

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Tarihi
0
Tarihin Masarautar Zazzau Da Sarakunanta (1)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban tushe mafi mahimmanci ga farkon tarihin Zazzau shine tarihin da aka kirkira a farkon karni na 20 daga al’adun baya.Yana ba da kuma labarin gargajiya ne na kafuwar masarautun kasar Hausa daga jarumin al’adu Bayajidda,kuma ya ba da jerin sunayen masu mulki tare da tsawon lokacin da kuma suka yi sarauta.Dangane da wannan tarihin, an ce asalin masarautar hausa ko Habe ta fara ne tun daga karni na 11, wanda Sarki Gunguma ya kafa. (1) Wannan majiyar kuma ta sanya ta zama daya daga jihohin Bakwai.

Mafi shaharar sarautar Zazzau ita ce Sarauniya (ko kuma Gimbiya) Amina, wacce ta yi mulki ko dai a tsakiyar karni na 15 da tsakiyar na 16, kuma Muhammed Bello ne ya rike ta, masanin tarihin Hausa a karni na 19 kuma Sarkin Musulmi na biyu, shine farkon wanda ya kafa daula a tsakanin Hausawa(2).

Zazzau ta kasance wurin tattara bayi ne don a kai su  zuwa kasuwannin Arewacin Kano da Katsina, inda ake musayar su da gishiri tare da ‘yan kasuwar da ke jigilar su zuwa Arewacin Sahara.(3) Dangane da tarihi a cikin littafin, an gabatar da addinin musulunci ga masarautar a wajen shekara ta 1456, amma ga alama ya bazu a hankali, kuma tsafin arna ya ci gaba har zuwa lokacin da Fulani suka ci shekara ta 1808.A wasu lokuta a tarihinta,Zazzau ta kasance tana karkashin kasashen makwabta irin su Songhai, Bornu da kuma Kwararafa.(4) Wannan karin rubutu da aka sa bai daidaitu  ba domin a kwai tsallaken zance a dukkanin sakin layin. Zazzagawa an same su da addinin musulunci kuma Shehu Usmanu ya tabbatar da hakan.Tun asali kasar Zazzau ba su da maguzawa.

Masarautar Gidan Fulani

A watan Disamba na shekara ta 1808 babu Fulani a cikin wadanda Shehu Usmanu Danfodiyo ya turo su da su kifar da ko su fidda Sarkin Zazzau Muhammadu Awwal Makau daga kasar Zazzau, illah kinibibin da ya kullu a tsakanin Malaman da suke zaune a kasar Zazzau.Wannan ya biyo bayan hijirar da Sarkin Kano Muhammadu Al-wali ya yi bayan kashe shararren Malamin nan malam Dan Zabuwa wanda ya ke shima bafillace ne. Ganin haka Fulani su kai gangami wajen tuntsurar da mulkinsa. Sarkin Kano ya yi kaura zuwa kasar Zazzau,a lokacin mulkin Sarkin Zazzau Muhammadu Awwal Makau a  cikin shekara ta 1807 amma bai samu hurumin zama ba. Duk da cewar shi suruki ne ya ke ga Sarkin Kano Muhammadu Al-wali.Wannan hijira ta Sarkin Kano

Labarai Masu Nasaba

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)

Muhammadu Al-wali  ita ta kawo cece-kuce a kasar Zazzau inda a karke ya kawo karken mulkin Sarkin Zazzau Muhammadu Awwal Makau. Inda gaurayen kabilun Malaman da ke zaune a kasar suka hada kai suka kifar da mulkinsa bayan ya tafi masallacin Idi don gabatar da  Karamar sallah .

Domin ta wannan dalilin ne ya sa shi tilasa ya bar kasar Zazzau inda ya kafa kasar Abuja kuma a halin yanzu ita ce aka kafa hedikwatar kasar nan.Kuma masarautar ta sauya da sunan sarki Sulaimanu Barau watau Suleja. Kalmar Fulani ta samu ne dalilin Shehu Usmanu.Amma malaman kabilun da ke zaune su ne: kabilar Mande a yau a na kiransu Mallawa,Barebari, Sullubawa da kuma Katsinawa.

Mun samo daga Wikipedia Hausa


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Abincin Da Ya Kamata Mai Azumi Ya Ci Da Wanda Bai Kamata Ba

Next Post

Nijeriya Ce Kan Gaba Wajen Lashe Kyaututtuka A Wasannin Kasashen Yammacin Afirika Na Bana

Related

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)
Tarihi

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

2 months ago
Tarihin Shugaban Ƙasar Mali Na Farko Sundiata Keita (2)
Tarihi

Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)

2 months ago
A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu
Tarihi

A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu

7 months ago
gusau
Tarihi

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (1)

11 months ago
A Tsame Masarautunmu Daga Siyasa
Al'adu

A Tsame Masarautunmu Daga Siyasa

12 months ago
Zazzau
Tarihi

Masarautar Argungu Da Al’adunta (1)

12 months ago
Next Post
Nijeriya Ce Kan Gaba Wajen Lashe Kyaututtuka A Wasannin Kasashen Yammacin Afirika Na Bana

Nijeriya Ce Kan Gaba Wajen Lashe Kyaututtuka A Wasannin Kasashen Yammacin Afirika Na Bana

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

Sin Na Maraba Da Kamfanonin Kasa Da Kasa Har Da Na Amurka 

May 28, 2025
Miƙa Mulki Daga Buhari Zuwa Tinubu: Abubuwan Da Suka Fi Jan Hankali

Tinubu Ya Yi Ƙoƙari, Gyaran Nijeriya Aikin Kowa Da Kowa Ne – Buhari

May 28, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya

May 28, 2025
Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

May 28, 2025
Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin 

May 28, 2025
Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama

May 28, 2025
Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 28, 2025
Gwamnatin Adamawa Ta Fitar Da Naira Biliyan 2.4 Domin Biyan Jarrabawar WAEC Da NECO

Adamawa Ta Amince Da Mafi Ƙarancin Albashi Na ₦70,000 Ga Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi 

May 28, 2025
Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya

Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya

May 28, 2025
An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC

An Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Ta Taron Kolin ASEAN-Sin-GCC

May 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.