• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron Ƙasashen Musulunci A Saudiya: Tinubu Ya Nemi A Kawo Ƙarshen Ta’addancin Isra’ila A Gaza

by Sulaiman
8 months ago
in Manyan Labarai
0
Taron Ƙasashen Musulunci A Saudiya: Tinubu Ya Nemi A Kawo Ƙarshen Ta’addancin Isra’ila A Gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci a kawo ƙarshen hare-haren ƙare-dangin da ƙasar Isra’ila yi wa Zirin Gaza, yana mai jaddada cewa tsawaita rikicin da take yi a Falasɗinu ya janyo wahala mai yawa.

 

Tinubu ya bayyana hakan ne a ranar Litinin a babban taron ƙasashen Larabawa da Musulmi da aka gudanar a Riyadh, babban birnin ƙasar Saudi Arebiya, inda shugabannin suka taru domin magance matsalar da ke ƙara ƙamari a yankin Gabas ta Tsakiya.

  • Taron Ƙasashen Musulunci A Saudiya: Tinubu Ya Nemi A Kawo Ƙarshen Ta’addancin Isra’ila A Gaza
  • ACF Ta Bukaci Sojoji Su Gaggauta Murkushe Lakurawa

A yayin da yake jawabi ga shugabannin Ƙungiyar Haɗin Kan Ƙasashen Musulmi (OIC) da Ƙungiyar Ƙasashen Larabawa, Tinubu ya bayyana goyon bayan Nijeriya na ganin an samar da maslaha tsakanin ƙasashen biyu.

 

Labarai Masu Nasaba

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Ya yi kira da a samar da wani ƙudiri da zai bai wa Isra’ila da Falasɗinawa damar zama tare cikin lumana da tsaro.

 

Ya ce: “Rikicin na Falasɗinu ya daɗe da daɗewa, yana jawo wahala mai yawa ga rayuka,” in ji shi.

 

Shugaban na Nijeriya ya jaddada cewa tofin Allah-tsine ake yi kan lamarin bai isa ba, yana mai kira ga shugabannin duniya da su tashi tsaye don kawo ƙarshen abin da Isra’ila ke aiwatarwa a Gaza.

 

Ya ce: “Babu wata manufa ta siyasa, da dabarun soji, da kuma matsalar tsaro da ya kamata ta kawo asarar rayuka da dama,” inji shi.

 

Ya yi kira ga dukkan ɓangarorin da ke rikici a Gabas ta Tsakiya da su kiyaye ƙa’idojin daidaito da haƙƙoƙin fararen hula a ƙarƙashin dokokin ƙasa da ƙasa.

 

Shugaban ya yaba wa Sarki Salman na Saudiyya da kuma Yarima mai jiran gado Mohammed bin Salman bisa kiran taron, yana mai bayyana shi a matsayin wata muhimmiyar dama ta sabunta yunƙurin diflomasiyya da ƙoƙarin samar da zaman lafiya mai ɗorewa.

 

Ya ba da tabbacin cewa Nijeriya za ta ci gaba da tallafa wa yunƙurin ƙasashen duniya na haɓaka zaman lafiya da kwanciyar hankali a Gabas ta Tsakiya.

 

Shugaba Tinubu ya buƙaci da a kafa sakatariyar da za ta aiwatar da ƙudirorin taron.

 

Ya buƙaci shugabannin da su umarci zaɓaɓɓun shugabannin gwamnatocin da su nemi tallafi a duniya da kuma sa ido kan aiwatar da ƙudirorin taron, tare da bayar da rahotanni a kai a kai ga shugabannin ƙungiyar OIC da na Ƙungiyar Ƙasashen Larabawa, har sai an samu zaman lafiya na dindindin a yankin Gabas ta Tsakiya.

 

A jawabin sa na buɗe taron, Yarima mai jiran gado na Saudiyya, Mohammed bin Salman, ya yi Allah-wadai da ta’addancin da Isra’ila ke yi a Gaza da Lebanon, da suka haɗa da kai hari kan fararen hula da kuma ci gaba da keta haddin masallacin Al-Aƙsa.

 

Ya kuma yi Allah-wadai da haramcin da Isra’ila ta yi wa Hukumar Ba da Agaji da Ayyuka ta amfani Majalisar Ɗinkin Duniya (UNRWA) daga kai kayan agaji ga Falasɗinawa da kuma raba al’ummar Lebanon da muhallin su da take yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaGazaIsra'ilawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Adadin Motoci Masu Amfani Da Sabbin Makamashi Da Aka Sayar A Sin Tsakanin Janairu Zuwa Oktoba Ya Kai Kusan Kaso 40%

Next Post

Wakilin Musamman Na Sin Game Da Batun Sauyin Yanayi Ya Yi Karin Haske Game Da Shigar Kasarsa Batun Shawo Kan Sauyin Yanayi

Related

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

4 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

7 hours ago
Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

17 hours ago
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

1 day ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

2 days ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

2 days ago
Next Post
Wakilin Musamman Na Sin Game Da Batun Sauyin Yanayi Ya Yi Karin Haske Game Da Shigar Kasarsa Batun Shawo Kan Sauyin Yanayi

Wakilin Musamman Na Sin Game Da Batun Sauyin Yanayi Ya Yi Karin Haske Game Da Shigar Kasarsa Batun Shawo Kan Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.