ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron Ƙasashen Musulunci A Saudiya: Tinubu Ya Nemi A Kawo Ƙarshen Ta’addancin Isra’ila A Gaza

by Sulaiman
2 years ago
Gaza

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci a kawo ƙarshen hare-haren ƙare-dangin da ƙasar Isra’ila yi wa Zirin Gaza, yana mai jaddada cewa tsawaita rikicin da take yi a Falasɗinu ya janyo wahala mai yawa.

 

Tinubu ya bayyana hakan ne a ranar Litinin a babban taron ƙasashen Larabawa da Musulmi da aka gudanar a Riyadh, babban birnin ƙasar Saudi Arebiya, inda shugabannin suka taru domin magance matsalar da ke ƙara ƙamari a yankin Gabas ta Tsakiya.

ADVERTISEMENT
  • Taron Ƙasashen Musulunci A Saudiya: Tinubu Ya Nemi A Kawo Ƙarshen Ta’addancin Isra’ila A Gaza
  • ACF Ta Bukaci Sojoji Su Gaggauta Murkushe Lakurawa

A yayin da yake jawabi ga shugabannin Ƙungiyar Haɗin Kan Ƙasashen Musulmi (OIC) da Ƙungiyar Ƙasashen Larabawa, Tinubu ya bayyana goyon bayan Nijeriya na ganin an samar da maslaha tsakanin ƙasashen biyu.

 

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Ya yi kira da a samar da wani ƙudiri da zai bai wa Isra’ila da Falasɗinawa damar zama tare cikin lumana da tsaro.

 

Ya ce: “Rikicin na Falasɗinu ya daɗe da daɗewa, yana jawo wahala mai yawa ga rayuka,” in ji shi.

 

Shugaban na Nijeriya ya jaddada cewa tofin Allah-tsine ake yi kan lamarin bai isa ba, yana mai kira ga shugabannin duniya da su tashi tsaye don kawo ƙarshen abin da Isra’ila ke aiwatarwa a Gaza.

 

Ya ce: “Babu wata manufa ta siyasa, da dabarun soji, da kuma matsalar tsaro da ya kamata ta kawo asarar rayuka da dama,” inji shi.

 

Ya yi kira ga dukkan ɓangarorin da ke rikici a Gabas ta Tsakiya da su kiyaye ƙa’idojin daidaito da haƙƙoƙin fararen hula a ƙarƙashin dokokin ƙasa da ƙasa.

 

Shugaban ya yaba wa Sarki Salman na Saudiyya da kuma Yarima mai jiran gado Mohammed bin Salman bisa kiran taron, yana mai bayyana shi a matsayin wata muhimmiyar dama ta sabunta yunƙurin diflomasiyya da ƙoƙarin samar da zaman lafiya mai ɗorewa.

 

Ya ba da tabbacin cewa Nijeriya za ta ci gaba da tallafa wa yunƙurin ƙasashen duniya na haɓaka zaman lafiya da kwanciyar hankali a Gabas ta Tsakiya.

 

Shugaba Tinubu ya buƙaci da a kafa sakatariyar da za ta aiwatar da ƙudirorin taron.

 

Ya buƙaci shugabannin da su umarci zaɓaɓɓun shugabannin gwamnatocin da su nemi tallafi a duniya da kuma sa ido kan aiwatar da ƙudirorin taron, tare da bayar da rahotanni a kai a kai ga shugabannin ƙungiyar OIC da na Ƙungiyar Ƙasashen Larabawa, har sai an samu zaman lafiya na dindindin a yankin Gabas ta Tsakiya.

 

A jawabin sa na buɗe taron, Yarima mai jiran gado na Saudiyya, Mohammed bin Salman, ya yi Allah-wadai da ta’addancin da Isra’ila ke yi a Gaza da Lebanon, da suka haɗa da kai hari kan fararen hula da kuma ci gaba da keta haddin masallacin Al-Aƙsa.

 

Ya kuma yi Allah-wadai da haramcin da Isra’ila ta yi wa Hukumar Ba da Agaji da Ayyuka ta amfani Majalisar Ɗinkin Duniya (UNRWA) daga kai kayan agaji ga Falasɗinawa da kuma raba al’ummar Lebanon da muhallin su da take yi.

Gaza
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Wakilin Musamman Na Sin Game Da Batun Sauyin Yanayi Ya Yi Karin Haske Game Da Shigar Kasarsa Batun Shawo Kan Sauyin Yanayi

Wakilin Musamman Na Sin Game Da Batun Sauyin Yanayi Ya Yi Karin Haske Game Da Shigar Kasarsa Batun Shawo Kan Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.