ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron Ƙasashen Musulunci A Saudiya: Tinubu Ya Nemi A Kawo Ƙarshen Ta’addancin Isra’ila A Gaza

by Sulaiman
2 years ago
Gaza

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya buƙaci a kawo ƙarshen hare-haren ƙare-dangin da ƙasar Isra’ila yi wa Zirin Gaza, yana mai jaddada cewa tsawaita rikicin da take yi a Falasɗinu ya janyo wahala mai yawa.

 

Tinubu ya bayyana hakan ne a ranar Litinin a babban taron ƙasashen Larabawa da Musulmi da aka gudanar a Riyadh, babban birnin ƙasar Saudi Arebiya, inda shugabannin suka taru domin magance matsalar da ke ƙara ƙamari a yankin Gabas ta Tsakiya.

ADVERTISEMENT
  • Taron Ƙasashen Musulunci A Saudiya: Tinubu Ya Nemi A Kawo Ƙarshen Ta’addancin Isra’ila A Gaza
  • ACF Ta Bukaci Sojoji Su Gaggauta Murkushe Lakurawa

A yayin da yake jawabi ga shugabannin Ƙungiyar Haɗin Kan Ƙasashen Musulmi (OIC) da Ƙungiyar Ƙasashen Larabawa, Tinubu ya bayyana goyon bayan Nijeriya na ganin an samar da maslaha tsakanin ƙasashen biyu.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

Ya yi kira da a samar da wani ƙudiri da zai bai wa Isra’ila da Falasɗinawa damar zama tare cikin lumana da tsaro.

 

Ya ce: “Rikicin na Falasɗinu ya daɗe da daɗewa, yana jawo wahala mai yawa ga rayuka,” in ji shi.

 

Shugaban na Nijeriya ya jaddada cewa tofin Allah-tsine ake yi kan lamarin bai isa ba, yana mai kira ga shugabannin duniya da su tashi tsaye don kawo ƙarshen abin da Isra’ila ke aiwatarwa a Gaza.

 

Ya ce: “Babu wata manufa ta siyasa, da dabarun soji, da kuma matsalar tsaro da ya kamata ta kawo asarar rayuka da dama,” inji shi.

 

Ya yi kira ga dukkan ɓangarorin da ke rikici a Gabas ta Tsakiya da su kiyaye ƙa’idojin daidaito da haƙƙoƙin fararen hula a ƙarƙashin dokokin ƙasa da ƙasa.

 

Shugaban ya yaba wa Sarki Salman na Saudiyya da kuma Yarima mai jiran gado Mohammed bin Salman bisa kiran taron, yana mai bayyana shi a matsayin wata muhimmiyar dama ta sabunta yunƙurin diflomasiyya da ƙoƙarin samar da zaman lafiya mai ɗorewa.

 

Ya ba da tabbacin cewa Nijeriya za ta ci gaba da tallafa wa yunƙurin ƙasashen duniya na haɓaka zaman lafiya da kwanciyar hankali a Gabas ta Tsakiya.

 

Shugaba Tinubu ya buƙaci da a kafa sakatariyar da za ta aiwatar da ƙudirorin taron.

 

Ya buƙaci shugabannin da su umarci zaɓaɓɓun shugabannin gwamnatocin da su nemi tallafi a duniya da kuma sa ido kan aiwatar da ƙudirorin taron, tare da bayar da rahotanni a kai a kai ga shugabannin ƙungiyar OIC da na Ƙungiyar Ƙasashen Larabawa, har sai an samu zaman lafiya na dindindin a yankin Gabas ta Tsakiya.

 

A jawabin sa na buɗe taron, Yarima mai jiran gado na Saudiyya, Mohammed bin Salman, ya yi Allah-wadai da ta’addancin da Isra’ila ke yi a Gaza da Lebanon, da suka haɗa da kai hari kan fararen hula da kuma ci gaba da keta haddin masallacin Al-Aƙsa.

 

Ya kuma yi Allah-wadai da haramcin da Isra’ila ta yi wa Hukumar Ba da Agaji da Ayyuka ta amfani Majalisar Ɗinkin Duniya (UNRWA) daga kai kayan agaji ga Falasɗinawa da kuma raba al’ummar Lebanon da muhallin su da take yi.

Gaza
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri
  • Sulaiman
    Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK
  • Sulaiman
    Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA
  • Sulaiman
    Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

MASU ALAKA

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna
Rahotonni

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah
Manyan Labarai

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

July 18, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Next Post
Wakilin Musamman Na Sin Game Da Batun Sauyin Yanayi Ya Yi Karin Haske Game Da Shigar Kasarsa Batun Shawo Kan Sauyin Yanayi

Wakilin Musamman Na Sin Game Da Batun Sauyin Yanayi Ya Yi Karin Haske Game Da Shigar Kasarsa Batun Shawo Kan Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah

July 18, 2026
Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

Tasirin Da VAR Ta Yi A Gasar Kofin Duniya

July 18, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.