• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron COP28: Ba Sharholiya Ce Ta Kai Tinubu Da Tawagarsa Dubai ba – Ministan Yada Labarai 

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Taron COP28: Ba Sharholiya Ce Ta Kai Tinubu Da Tawagarsa Dubai ba – Ministan Yada Labarai 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ba yawon sharholiya ce ta kai Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ‘yan tawagarsa a taron Majalisar Ɗinkin Duniya kan sauyin yanayi da ake yi a Dubai ba, kowa da aikin da zai yi a yayin taron.

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris ne ya bayyana hakan acikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai inda ya yi raddi kan masu zargin gwamnatin tarayya da fita da mutane fiye da kima zuwa taron na COP28 da ya gudana a kasar Dubai.

  • Sin Ta Sake Zama Memba A Rukunin A A Kungiyar IMO
  • Kasar Sin: Yawan Kunshin Kayayyaki Da Aka Isar A Kasar Ya Kafa Wani Sabon Tarihi

Idris ya ce gwamnati ta lura da maganganun da ake yi kan adadin ‘yan tawagar da su ka je Dubai domin halartar taron, kuma ta ga “akwai buƙatar ta samar da ƙarin haske kamar yadda ta yi alƙawarin za ta riƙa gudanar da al’amuran ta a bayyane tare da kasancewa mai fayyace komai ga jama’a dangane da abin da ya ke bukatar karin haske”

A cewarsa, “Taron Masu Ruwa da Tsaki (Convention of Parties, COP) na Tsarin Shirye-shiryen Majalisar Ɗinkin Duniya kan Sauyin Yanayi, ‘UNFCCC’ shi ne mashahurin Taron Duniya kan Sauyin Yanayi wanda a bana ya samu halartar fiye da mutane 70,000 daga kasashe fiye da 100. Wakilcin da Nijeriya ta samu ya yi daidai da matsayinta na jagora mai faɗa a ji a Nahiyar Afirka kuma babbar mai taka rawa kan al’amarin sauyin yanayi, wato ‘climate action’.”

Ya ce waɗanda su ka halarci taron daga Nijeriya sun haɗa da jami’an gwamnati, wakilan ‘yan kasuwa da na ƙungiyoyi masu zaman kansu, da ‘yan sa kai, gwamnatocin jihohi, ‘yan jarida, hukumomin ƙasa da ƙasa, wakilan al’ummomin da sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Idris ya bada lissafin ‘yan tawagar da su ka je a aljihun gwamnati su mutum 422, kamar haka:

idris ya bayyana cewa, Mutane 422 ne kacal suka halarci taron acikin aljihun gwamnati. Wadanda suka hada da Hukumar Sauyin Yanayi ta Ƙasa, 32; Ma’aikatar Muhalli ta Tarayya, 34; Dukkan Ma’aikatu, 167; Fadar Shugaban Ƙasa, 67; Ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa, 9; Majalisar Tarayya, 40 sai kuma Hukumomin gwamnati da cibiyoyi, 73.

 

Ya bada tabbacin cewa a matsayin Nijeriya na wadda ta ke da ƙarfin tattalin arziki fiye da sauran ƙasashen Afrika kuma mafi yawan jama’a a nahiyar, kuma ta na da tattalin arziki da ake samu daga ma’adinai, wadda ke fuskantar barazanar sauyawar yanayi, ta na da muhimmin matsayi a batun sauyin yanayi, “don haka rawar da za mu taka a taron CCOP28 ba kaɗan ba ce.”

Ministan ya ƙara da cewa: “Taron COP28 ya bada damarmaki na zuba jari da ƙulla yarjejeniyoyin haɗin gwiwa a sassa daban-daban da sauyin yanayi ya shafe su, kuma yanzu haka Nijeriya ta fara cin moriyar shiga taron da ta yi, kamar yadda waɗannan al’amurran su ka shaida:

“Nijeriya da Jamus sun rattaba hannu kan gaggauta aiwatar da Shirin Shugaban Ƙasa kan Wutar Lantarki (PPI) domin inganta samar da lantarki a Nijeriya.

“Shugaba Tinubu ya jagoranci wani babban taro wanda masu ruwa da tsaki da masu zuba jari su ka yi kan Kasuwar Man Fetur ta Nijeriya da Shirin Kawo Motocin Sufuri masu aiki da hasken Rana a lokacin da ake taron ƙoli na COP28 kan sauyin yanayi.

“Akwai alamun Nijeriya za ta ci moriyar Asusun Asara Da Ɓarna (Loss and Damage Fund) wanda aka kafa a lokacin taron COP27 da aka yi a Masar kuma aka ƙaddamar da shi a wajen buɗe wannan taron na COP28 a Dubai. Asusun zai samar da kuɗaɗen da ba bashi ba ne waɗanda za a kashe don tallafa wa ƙasashen da tasirin sauyin yanayi ya fi shafarsu.

“Haka kuma, Shugaban Ƙasa ya yi taro da Shugaban Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE) don tabbatar da yarjejeniyoyin da ke akwai a tsakanin ƙasashen biyu. Duk wannan ban da fa tattaunawar diflomasiyya da aka yi da ƙasashe da ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa daban-daban.”

“Ya kamata a sani cewa, a tsawon shekaru, Nijeriya ta tabbatar da matsayin ta kan batun sauyin yanayi ta hanyar zama ƙasar Afrika ta farko da ta ƙaddamar da Tsarin Tafiyar da Makamashi (Energy Transition Plan), kuma ƙasar Afrika ta farko da ta fitar da Dukiyar Ƙasa Kan Daina Amfani da Makamashin Mai (Sovereign Green Bond), sannan ta na cikin ƙasashe na farko da su ka kafa dokar sauyin yanayi ta ƙasa.

“Saboda haka, muka fitar da wannan karin haske game da cece-kucen da ake yi na tafiya da mutane fiye da kima zuwa taron COP28, Shugaba Tinubu da sauran jami’an Gwamnatin Tarayya sun je Dubai ne domin gudanar da aiki tukuru ba sharholiya ba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: COP28Tawagar Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Abubuwa 5 Da Jam’iyyatu Ansariddeen Attijjaniyya Ta Nemi Gwamnati Ta Yi Kan Kan Kisan ‘Yan Maulidi A Kaduna 

Next Post

An Bayyana Rawar Da Kasar Sin Ta Taka Kan Sauyin Yanayi Yayin Taron COP28

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

3 hours ago
COP28
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

4 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

7 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

10 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

11 hours ago
Next Post
An Bayyana Rawar Da Kasar Sin Ta Taka Kan Sauyin Yanayi Yayin Taron COP28

An Bayyana Rawar Da Kasar Sin Ta Taka Kan Sauyin Yanayi Yayin Taron COP28

LABARAI MASU NASABA

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
COP28

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.