• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron JKS: Kudurin Kara Zurfafa Gyare-gyare Zai Sa Kaimin Aikin Zamanintar Da Sin

by Abdulrazaq Yahuza
11 months ago
in Ra'ayi Riga
0
Taron JKS: Kudurin Kara Zurfafa Gyare-gyare Zai Sa Kaimin Aikin Zamanintar Da Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Na fara sanin manufar gyare-gyare da bude kofa ta kasar Sin a lokacin da aka yi bikin cikar manufar shekaru 40 da kafuwa a shekarar 2018. Rahotannin da na gani a game da ci gaban da manufar ta kawowa kasar da sauran kasashen da aka yi kawancen ci gaba tare da su, a karkashin tsare-tsare daban-daban kamar na Ziri Daya da Hanya Daya (BRI), Dandalin Kawance na FOCAC, sun nuna kyakkyawar alkiblar da Sin ta dosa.

Manufar wadda a bana ta cika shekaru 46 da kafuwa ta kara samun tagomashi yayin da zaman taro na uku na Kwamitin Kolin Jam’iyyar Kwaminisanci ta Kasar Sin (JKS) karo na 20 ya amince da kudurin kara zurfafa gyare-gyare don habaka zamanintar da kasar, a birnin Beijing, kwanan nan.
Babban burin da ake neman cimmawa a kokarin da ake na kara zurfafa gyare-gyare, shi ne ci gaba da ingantawa da raya tsarin gurguzu mai sigar musamman ta kasar Sin, da kuma zamanintar da tsarin gudanarwa na Sin da karfin iya shugabanci.

Da yake masu magana kan ce “aiki ga mai kare ka”, ana sa ran nan da 2035, Sin za ta kammala gina tattalin arzikin kasuwanci irin na gurguzu mai matukar inganci a dukkan fannoni. Tabbas hakar kasar za ta cimma ruwa bisa yadda ta sha damarar ganin an sauke duk wani nauyi da ya rataya ga samun nasarar kudurin a yayin da Jamhuriyar Jama’ar Kasar Sin za ta yi bikin cikarta shekara 80 da kafuwa a 2029.

Ba kanta kadai take kallo ba, a duk harkokin ci gaba da wayewa irin na zamani mai inganci da babu coge a ciki, kasar Sin tana duba al’ummar duniya a matsayin wadanda za a gudu tare, a tsira tare. Shi ya sa, sanarwar bayan taron JKS ta jaddada cewa, tsarin zamanintar Sin shi ne tsarin bunkasa zaman lafiya a zamanance, domin “a huldar dake tsakanin kasashen waje da kasar Sin, kasar ta tsaya tsayin daka wajen aiwatar da manufar zaman lafiya mai cin gashin kanta, kana ta himmatu wajen inganta al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya,” in ji sanarwar.

A aikace, an ga irin kokarin da Sin take yi a manufofinta na bude kofa da zaman lafiyar duniya ta hanyar kai ci gaban tattalin arziki maimakon tayar da husumar yake-yake a kasashe daban-daban da kuma jawo su a jiki su shigo cikinta domin cin moriyar juna. Wannan ya tsayawa kasashen yamma a kahon zuci, shi ya sa duk abin da kasar ta kawo sai an shafa masa kashin kaji ta hanyar kushe manufar bude kofar da kuma yayata farfaganda a kafafen yada labarunsu daban-daban cewa, manufar tana samun koma-baya da rashin karbuwa a duniya.

Labarai Masu Nasaba

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

To sai dai, a gaya musu “kifi na ganin ka mai jar koma”, domin kasar Sin ta ci gaba da rike kambunta na zama kasa ta biyu mafi karfin tattalin arziki a duniya da zama kasar da ta fi yawan cinikin hajjoji a cikin shekaru bakwai a jere, da ci gaban da ta samu na hada-hadar tattalin arzikin cikin gida a rabin farko na bana da ya kai fiye da Yuan tiriliyan 61, wanda ya karu da kashi 5 idan aka dora a sikeli da na bara war haka.

Bisa jajircewar Sin a karkashin shirinta na bude kofa na zamani, ta ci gaba da fadada huldar kasuwanci da kasashen duniya. Kasuwancin da take yi a karkashin hadin gwiwar shawarar Ziri Daya da Hanya Daya (BRI) ya karu da kashi 7.2, a rabin shekarar 2024.

Bayan haka, Sin ta kara yawan kasashen da take sahale musu shiga cikinta ba tare da biza ba. A tsakanin wata shida na 2024 kacal, a kalla ’yan kasashen waje miliyan 14 suka shigo cikinta, kusan adadin da ya ninka wadanda suke shiga duk shekara.

Wadannan misalai sun isa su nuna karbuwar da manufar bude kofar Sin ke samu tare da fadada damammakin zuba jari ga ’yan kasashen waje a cikinta.

A bisa tsare-tsaren kara zurfafa gyare-gyare da taron JKS ya aminta da su, tabbas ba Sin kadai za ta ci gajiyar wadannan gyare-gyare ba har da sauran kasashen duniya bisa manufarta ta bude kofa, ba kamar masu tsuke kasuwanninsu na shigo da kaya da fadada na fitarwa kamar yadda su Amurka ke yi ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: bude kofaCi Gabagyare-gyareJKSSinTaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kama Wanda Ya Kitsa Kashe Janar Udokwere A Kano

Next Post

Kamfe: An Tara Wa Kamala Haris Kusan Dala Miliyan 50 Cikin Sa’o’i 2 A Amurka

Related

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

1 day ago
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba
Ra'ayi Riga

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

3 days ago
Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Ra'ayi Riga

Daga Xi’an Zuwa Astana: Me Muka Koya Daga Taron Kolin Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

1 week ago
Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta
Ra'ayi Riga

Yafe Harajin Fito: Kasar Sin Na Cika Alkawarinta

1 week ago
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada
Ra'ayi Riga

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

1 week ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

2 weeks ago
Next Post
Kamfe: An Tara Wa Kamala Haris Kusan Dala Miliyan 50 Cikin Sa’o’i 2 A Amurka

Kamfe: An Tara Wa Kamala Haris Kusan Dala Miliyan 50 Cikin Sa'o'i 2 A Amurka

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Cimma Nasarar Yin Tattaki A Waje Karo Na 2

June 27, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador

June 27, 2025
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

June 27, 2025
WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

WAEC Na Buƙatar Kwaskwarima

June 27, 2025
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

June 27, 2025
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

June 27, 2025
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

June 27, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

Gwamnan Kaduna Ya Yunkura Don Warware Matsalolin Rashin Aikin Yi Ga Matasa – Dan Isan

June 27, 2025
Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

Sojojin Sama Sun Yi Lugudan Wuta Kan Ƴan Ta’adda A Jihar Neja

June 27, 2025
2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.