• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tashar Qausain TV Ta Karrama Pantami Da Lambar Yabo

by Leadership Hausa
2 years ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Tashar Qausain TV Ta Karrama Pantami Da Lambar Yabo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An karrama Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami da lambar yabo, mako biyu bayan kammala aiki a Gwamnatin Muhammadu Buhari.

Fitacciyar tashar Talabijin ta Qausain TV ta mika lambar yabon ga tsohon ministan a yayin ziyarar da shugabannin tashar suka kai masa a gidansa dake Abuja.

A yayin ba da lambar yabon, Shugaban Tashar, Nasir Musa Albani Agege ya bayyana Isa Ali Pantami a matsayin wata kadara ta Nijeriya, wanda ya ce sun yi la’akari da cancanta ne zalla sakamakon namijin kokarin da tsohon ministan ya nuna wajen inganta bangaren Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani a lokacin da yake ofis.

Yana mai cewa, Pantami ya fidda Nijeriya kunya ta fuskar aiwatar da manyan tsare-tsaren wadanda suka dora kasar a tafarkin cigaba mai dorewa.

“Kazalika wannan lambar jinjina ce ga irin daruruwan cigaba da mai girma tsohon ministan ya samar a fannin sadarwar zamani da habaka tattalin arzikin zamani a Najeriya” In ji Albani.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

A yayin da yake karbar lambar yabon, Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami ya gode wa Qausain TV bisa zakulo shi a bisa gudumawar da ya bayar a wannan fanni na sadarwar zamani.

Haka kuma ya yaba da irin jajircewar tashar ta Qausain TV wajen amfani da nagartattun kayan aiki da kuma sadaukarwa wajen ilmantar da al’ummar Najeriya da wajenta kusan shekara uku da suka gabata.

Ya ce “Hakika na san Qausain TV a matsayin tashar Talabijin da ke yada shirye-shiryenta a tauraron Dan Adam, wadda miliyoyin mutane ke kallonta, musamman saboda kyawawan shirye-shirye cikin harsunan Hausa, Turanci da kuma Larabci.”

“Kamar kuma yadda na san shi kansa shugaban tashar, wato Albani shekaru da yawa. Na san irin jajircewarsa wajen fasaha da kirkira. Shi ne ma Dan Nijeriya na farko da na sani wanda ya fara kirkirar Manhaja a kan Play Store da kuma Apple,” In ji Isa Pantami.

  • Kungiya Ta Yaba Wa Shugaba Tinubu Kan Inganta Tsaro Da Yaki Da Rashawa

 

A daidai lokacin da yake taya Shugaban Qausain murnar wannan nasarar da ya samu cikin kankanin lokaci, sannan ya shawarci matasa da su yi koyi da shi domin cigaban kasarmu Najeriya.

Baya ga tawagar Qausain TV da suka bada lambar yabon, kwarkwaryar taron ya samu halartar Yan’uwa da abokan arziki na tsohon ministan a gidansa dake Abuja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KarramawaPantamiqausain tvYabo
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hade-haden Lemo Mai Dandano

Next Post

Yadda Ake Wanke Bandaki da Coca-cola

Related

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

5 hours ago
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
Manyan Labarai

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

6 hours ago
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

8 hours ago
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
Manyan Labarai

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

10 hours ago
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
Ra'ayi Riga

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

10 hours ago
Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara

12 hours ago
Next Post
Yadda Ake Wanke Bandaki da Coca-cola

Yadda Ake Wanke Bandaki da Coca-cola

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

June 26, 2025
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

June 26, 2025
Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.