• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tashar Qausain TV Ta Karrama Pantami Da Lambar Yabo

by Leadership Hausa
2 years ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Tashar Qausain TV Ta Karrama Pantami Da Lambar Yabo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An karrama Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami da lambar yabo, mako biyu bayan kammala aiki a Gwamnatin Muhammadu Buhari.

Fitacciyar tashar Talabijin ta Qausain TV ta mika lambar yabon ga tsohon ministan a yayin ziyarar da shugabannin tashar suka kai masa a gidansa dake Abuja.

A yayin ba da lambar yabon, Shugaban Tashar, Nasir Musa Albani Agege ya bayyana Isa Ali Pantami a matsayin wata kadara ta Nijeriya, wanda ya ce sun yi la’akari da cancanta ne zalla sakamakon namijin kokarin da tsohon ministan ya nuna wajen inganta bangaren Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani a lokacin da yake ofis.

Yana mai cewa, Pantami ya fidda Nijeriya kunya ta fuskar aiwatar da manyan tsare-tsaren wadanda suka dora kasar a tafarkin cigaba mai dorewa.

“Kazalika wannan lambar jinjina ce ga irin daruruwan cigaba da mai girma tsohon ministan ya samar a fannin sadarwar zamani da habaka tattalin arzikin zamani a Najeriya” In ji Albani.

Labarai Masu Nasaba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

A yayin da yake karbar lambar yabon, Tsohon Ministan Sadarwa da Tattalin Arziki na Zamani, Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami ya gode wa Qausain TV bisa zakulo shi a bisa gudumawar da ya bayar a wannan fanni na sadarwar zamani.

Haka kuma ya yaba da irin jajircewar tashar ta Qausain TV wajen amfani da nagartattun kayan aiki da kuma sadaukarwa wajen ilmantar da al’ummar Najeriya da wajenta kusan shekara uku da suka gabata.

Ya ce “Hakika na san Qausain TV a matsayin tashar Talabijin da ke yada shirye-shiryenta a tauraron Dan Adam, wadda miliyoyin mutane ke kallonta, musamman saboda kyawawan shirye-shirye cikin harsunan Hausa, Turanci da kuma Larabci.”

“Kamar kuma yadda na san shi kansa shugaban tashar, wato Albani shekaru da yawa. Na san irin jajircewarsa wajen fasaha da kirkira. Shi ne ma Dan Nijeriya na farko da na sani wanda ya fara kirkirar Manhaja a kan Play Store da kuma Apple,” In ji Isa Pantami.

  • Kungiya Ta Yaba Wa Shugaba Tinubu Kan Inganta Tsaro Da Yaki Da Rashawa

 

A daidai lokacin da yake taya Shugaban Qausain murnar wannan nasarar da ya samu cikin kankanin lokaci, sannan ya shawarci matasa da su yi koyi da shi domin cigaban kasarmu Najeriya.

Baya ga tawagar Qausain TV da suka bada lambar yabon, kwarkwaryar taron ya samu halartar Yan’uwa da abokan arziki na tsohon ministan a gidansa dake Abuja.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KarramawaPantamiqausain tvYabo
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hade-haden Lemo Mai Dandano

Next Post

Yadda Ake Wanke Bandaki da Coca-cola

Related

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba
Manyan Labarai

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

42 minutes ago
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara
Labarai

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

3 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

4 hours ago
Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?
Manyan Labarai

Shugabanci A Nijeriya: A Ina Ne Gizo Ke Saƙar?

4 hours ago
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri
Labarai

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

7 hours ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

9 hours ago
Next Post
Yadda Ake Wanke Bandaki da Coca-cola

Yadda Ake Wanke Bandaki da Coca-cola

LABARAI MASU NASABA

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana

September 14, 2025
Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

Za A Kaddamar Da Fim Mai Taken 731 A Sassan Duniya

September 14, 2025
Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

Lauyoyi Biyu Sun Janye Daga Kai Jaafar Jaafar Ƙara, Sun Ce An Sanya Sunayensu Ba Bisa Ƙa’ida Ba

September 14, 2025
Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

Kasar Sin Na Samarwa Duniya Damammaki A Fannin Hada-hadar Ba Da Hidima

September 14, 2025
Duba Ga KwaÉ—ayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

Duba Ga KwaÉ—ayi Da Son Duniya A Tsakanin Matan Wannan Zamanin

September 14, 2025
Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

Jagororin Kamfanonin Ketare Sun Nuna Gamsuwa Dangane Da Zuba Jari A Kasar Sin

September 14, 2025
Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

Bayan Fara Kamen Mabarata, An Samu Dalar Amurka, Wuƙa A Kwara

September 14, 2025
Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

September 14, 2025
An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

An Kammala Baje Kolin Hada-Hadar Cinikayyar Hidimomi Na Sin Na Shekarar 2025

September 14, 2025
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Sanar Da Dalilin Korar Hadimin Shettima Kan Bunƙasa Tattalin Arziƙi

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.