• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tashar Sararin Samaniyar Sin Za Ta Kasance “Gida Cikin Sararin Samaniya” Ga Dukkanin Bil Adama

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Tashar Sararin Samaniyar Sin Za Ta Kasance “Gida Cikin Sararin Samaniya” Ga Dukkanin Bil Adama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da misalin karfe 3 da minti 37 na yammacin jiya Litinin 31 ga watan Oktoba, kasar Sin ta yi nasarar harba bangare na uku, na tashar binciken sararin samaniyarta da ake kira Mengtian zuwa sararin samaniya.

Sa’an nan, bayan kimanin minti 8, dakin gwaje-gwaje na Mengtian ya rabu da rokar Long March-5B, ya kuma shiga hanyarsa kamar yadda aka tsara.

  • Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Makarantar ‘Family Support Programme’ Ta Shirya Taron Lakcoci Ga Ɗalibai Sama Da 100 A Katsina

Lamarin da ya nuna cewa, yawan dakunan gwaje-gwaje na tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin, sun karu daga guda biyu zuwa guda uku, wadanda za su kasance tamkar “siffar T”, matakin dake kara kusanto ga aikin kammala tashar.

Aikin gina tashar binciken sararin samaniyar ya kasance muhimmin mataki a aikin sararin samaniyar kasar Sin, inda kasar Sin ke tsayawa tsayin daka wajen raya aikin bisa manufofin amfani da albarkatun sararin samaniya ta hanyar zaman lafiya, da nuna adalci don cimma moriyar juna, da kuma bunkasa harkokin dake da nasaba da hakan cikin hadin gwiwa.

Kana, cikin tarihin bil Adama, tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin, ita ce tasha ta farko da aka bude ga dukkanin mambobin MDD.

Labarai Masu Nasaba

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

A halin yanzu, kasar Sin ta bayar da izinin yin gwaje-gwaje a tasharta ga shirye-shirye guda 9, da kasashe guda 17, da kamfanoni guda 23. Lamarin da ya nuna aniyar kasar Sin ta inganta dunkulewar dukkanin bil Adama a fannin habaka aikin sararin samaniya.

Albarkatun sararin samaniya sun zama albarkatu ga dukkanin bil Adama, ya kamata a yi amfani da su wajen tallafawa dukkanin bil Adama. Bayan an kammala aikin gina tashar binciken sararin samaniyar kasar Sin, za a shiga matakin amfani, da kuma raya tashar na tsawon shekaru 10.

Kana, kafin karshen shekarar bana, kasar Sin za ta kuma harba kumbo mai dauke da kayayyaki na Tianzhou mai lamba 5, da kumbo mai dauke da mutane na Shenzhou mai lamba 15, ta yadda ’yan sama jannati guda 6 za su yi aiki tare cikin tashar.

Ana da imanin cewa, a nan gaba, tashar binciken sararin samaniyar kasar Sin za ta kasance “sabon gida cikin sararin samaniya” ga dukkanin bil Adama, inda za su gudanar da aikin binciken sararin samaniya cikin hadin gwiwa.

Cikin tashar, ’yan sama jannati na kasar Sin da na kasashen waje, za su ba da gudummawar binciken sararin samaniya cikin hadin gwiwa, yayin da ake karfafa aikin yin amfani da albarkatun sararin samaniya cikin lumana. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Kebbi Ya Umarci A Biya Biliyan 2 Kudin Hutun Ma’aikata 

Next Post

EFCC Ta Cafke Wani Dan Siyasa Da Wasu Kan Satar Kudin Banki N1.4bn A Jihar Kogi

Related

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

20 hours ago
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

21 hours ago
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12
Daga Birnin Sin

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

22 hours ago
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

23 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

24 hours ago
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

1 day ago
Next Post
EFCC Ta Cafke Wani Dan Siyasa Da Wasu Kan Satar Kudin Banki N1.4bn A Jihar Kogi

EFCC Ta Cafke Wani Dan Siyasa Da Wasu Kan Satar Kudin Banki N1.4bn A Jihar Kogi

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.