• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tashar Sararin Samaniyar Sin Za Ta Kasance “Gida Cikin Sararin Samaniya” Ga Dukkanin Bil Adama

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Tashar Sararin Samaniyar Sin Za Ta Kasance “Gida Cikin Sararin Samaniya” Ga Dukkanin Bil Adama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da misalin karfe 3 da minti 37 na yammacin jiya Litinin 31 ga watan Oktoba, kasar Sin ta yi nasarar harba bangare na uku, na tashar binciken sararin samaniyarta da ake kira Mengtian zuwa sararin samaniya.

Sa’an nan, bayan kimanin minti 8, dakin gwaje-gwaje na Mengtian ya rabu da rokar Long March-5B, ya kuma shiga hanyarsa kamar yadda aka tsara.

  • Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Makarantar ‘Family Support Programme’ Ta Shirya Taron Lakcoci Ga Ɗalibai Sama Da 100 A Katsina

Lamarin da ya nuna cewa, yawan dakunan gwaje-gwaje na tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin, sun karu daga guda biyu zuwa guda uku, wadanda za su kasance tamkar “siffar T”, matakin dake kara kusanto ga aikin kammala tashar.

Aikin gina tashar binciken sararin samaniyar ya kasance muhimmin mataki a aikin sararin samaniyar kasar Sin, inda kasar Sin ke tsayawa tsayin daka wajen raya aikin bisa manufofin amfani da albarkatun sararin samaniya ta hanyar zaman lafiya, da nuna adalci don cimma moriyar juna, da kuma bunkasa harkokin dake da nasaba da hakan cikin hadin gwiwa.

Kana, cikin tarihin bil Adama, tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin, ita ce tasha ta farko da aka bude ga dukkanin mambobin MDD.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

A halin yanzu, kasar Sin ta bayar da izinin yin gwaje-gwaje a tasharta ga shirye-shirye guda 9, da kasashe guda 17, da kamfanoni guda 23. Lamarin da ya nuna aniyar kasar Sin ta inganta dunkulewar dukkanin bil Adama a fannin habaka aikin sararin samaniya.

Albarkatun sararin samaniya sun zama albarkatu ga dukkanin bil Adama, ya kamata a yi amfani da su wajen tallafawa dukkanin bil Adama. Bayan an kammala aikin gina tashar binciken sararin samaniyar kasar Sin, za a shiga matakin amfani, da kuma raya tashar na tsawon shekaru 10.

Kana, kafin karshen shekarar bana, kasar Sin za ta kuma harba kumbo mai dauke da kayayyaki na Tianzhou mai lamba 5, da kumbo mai dauke da mutane na Shenzhou mai lamba 15, ta yadda ’yan sama jannati guda 6 za su yi aiki tare cikin tashar.

Ana da imanin cewa, a nan gaba, tashar binciken sararin samaniyar kasar Sin za ta kasance “sabon gida cikin sararin samaniya” ga dukkanin bil Adama, inda za su gudanar da aikin binciken sararin samaniya cikin hadin gwiwa.

Cikin tashar, ’yan sama jannati na kasar Sin da na kasashen waje, za su ba da gudummawar binciken sararin samaniya cikin hadin gwiwa, yayin da ake karfafa aikin yin amfani da albarkatun sararin samaniya cikin lumana. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Kebbi Ya Umarci A Biya Biliyan 2 Kudin Hutun Ma’aikata 

Next Post

EFCC Ta Cafke Wani Dan Siyasa Da Wasu Kan Satar Kudin Banki N1.4bn A Jihar Kogi

Related

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

3 hours ago
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

4 hours ago
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

5 hours ago
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar
Daga Birnin Sin

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

6 hours ago
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha
Daga Birnin Sin

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

7 hours ago
Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6
Daga Birnin Sin

Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6

8 hours ago
Next Post
EFCC Ta Cafke Wani Dan Siyasa Da Wasu Kan Satar Kudin Banki N1.4bn A Jihar Kogi

EFCC Ta Cafke Wani Dan Siyasa Da Wasu Kan Satar Kudin Banki N1.4bn A Jihar Kogi

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

Abin Da Ya Sa NPA Da Kwalejin MAN Oron Suka Yi Haɗin Gwiwa

August 1, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

August 1, 2025
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

August 1, 2025
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

August 1, 2025
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Dimokuraɗiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

August 1, 2025
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

August 1, 2025
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

August 1, 2025
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

August 1, 2025
Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

Ministan Tsaron Kasar Sin Ya Nanata Shan Damarar PLA A Kan Sake Hadewar Kasar

August 1, 2025
An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

An Bude Atisayen “Hadin Gwiwa Na Teku Na 2025″ Tsakanin Sin Da Rasha

August 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.