• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tasirin Mata A Harkar Hakar Ma’adanai Na Kara Bayyana

by Bello Hamza
2 years ago
in Tattalin Arziki
0
Tasirin Mata A Harkar Hakar Ma’adanai Na Kara Bayyana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ci gaba da kokarin ganin ba a bar su a baya ba, wasu gungun mata a karkashin inuwar kungiyar ‘Women in Mining in Nigeria (WIMIN)’ sun kafa reshe na 27 a yankin Babban Birnin Tarayya Abuja don shiga a dama da su a harkar hakar ma’adanai a fadin kasar nan.

A bikin kaddamar da shugabanin reshen na Abuja da aka yi a karshen mako, Shugabar kungiyar ta kasa, Dakta Janet Adeyemi, ta ranstar da kwamitin riko wanda Dakta Comfort Asokoro-Ogaji, za ta jagoranta kafin a kai ga zaban shugabanin kungiyar na dindindin.

  • Kungiyar Kasar Sin Ta Lashe Dukkan Lambobin Zinare Na Wasannin Nutso A Gasar Wasannin Kasashen Asiya
  • Barazanar Tsaro: Gwamna Kefas Ya Nemi A Tura Masa Bataliya Zuwa Taraba

A jawabinta a wajen taron, Shugabar kungiyar na kasa, Hon Adeyemi, wadda mai ilimin ma’adanai ne kuma tsohuwar ‘yar majalisar kasa ce, ta bayyana cewa, ta kafa kungiyar ce bayan da ta lura da yadda ake cutar da mata a harkar ma’adanai a Nijeriya, musamman a wuraren hakar ma’adanai na Jos da saurar sassan kasar nan, kuma ana nisantar da su daga shiga cikin harkokin kasuwancin ma’adanai a kasar nan, haka kuma ta fahimci cewa, kwararrun mata masu ilimin hakar ma’adanai na fuskantar wariya ana kuma kange su daga rike mukamai a cibiyoyi da hukumomin gudanar da harkokin ma’adanai na kasa, a kan haka ta kudiri aniyar dawo da martabar mata a harkar hakar ma’adanai a Nijeriya.

Ta kara da cewa, da farko, ta fuskanci turjiya daga maza amma ganin yadda ta dake da aiwatar da kudurinta, a halin yanzu an samu mata da dama da ke aiki a bangaren ma’adanai har an kai ga kafa reshen kungiyar a jihohi 27 cikin jihohi 36 da yankin babbar birnin tarayya, akwai kuma reshen kungiyar a kasashen Afirika da wasu sassan duniya har guda 96.

Ta kuma kara da cewa, in har mata suka hada kai a tsakaninsu, maza ba za su iya zarce su ba, musamman ganin harkar ma’adanai na da bangarori daban-daban da kowa zai iya samun nashi alharin ba tare da takurawa wai ba, tun daga masu haka, sarrfawa da saye da sayarwa da kuma fitarwa kasashen waje.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

A nata jawabin, shugabar kungiyar na yankin Abuja, Dakta Comfort Asokoro-Ogaji, ta ce, za ta tabbatar da amfani da matsayinta wajen bunkasa shigar mata a harkar hakar ma’adanai a yankin Abuja.

A tattaunawar da ta yi da manema labarai, ta ce, Allah ya albarkaci yankin Abuja da ma’adanai masu muhimmanci wadanda suka hada da ‘Gold, Cassiterite, Dolomite, Lead/zinc, Marble da Tantalite’.

Ta yaba wa hukumar yankin babbar birnin Abuja a kan yadda ta kirkiro da sashin na musamman don kula da harkokin ma’adanai wanda hakan zai taimaka a gaggauta samar da aikin yi da arziki ga al’umma.

Dakta Asokoro-Ogaji ta kara da cewa, “A mastayin mu na mata za mu bayar da namu gudummawar wajen aiki a bangaren hakar ma’adanai tare da tabbatar da gwamnati na samun kudaden shiga daga bangaren hakar ma’adanai kamar yadda ya kamata.

“Ya kamata mata a yankjin Abuja su amfana da wadannan albarkatun kasa da Allah ya samar a yankin. Tabbas akwai abubuwan da suke bukatar kudi amma wasu abubuwan suna bukatar jajircewa ne kawai na al’umma, idan kowa ya bayar da nasa gudummawar dole a kai ga ci gaba wanda kuma hakan zai amfanar da al’umma gaba daya.

Bincike ya nuna cewa, mata na bayar da gaggrumin gudumawa a harkar hakar ma’adanai, amma ana amfani dasu ne kawai ba tare da suna cin cikakkiyar gajiyar aikin da suke yi ba. A kan haka aka nemi shugabannin al’umma sarakuna da sauran masu ruwa da tsaki da su tsayu wajen ganin dukkan al’umma na cin gajiyar ma’adanai da Allah ya horewa kasa, ta hanyar amfani da kudaden da ake samu wajen gudanar da ayyuykan ci gaba ga al’umma tare da sa ido don kare muhalli daga cutarwar ayyukan masu hakar ma’adanai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisa Za Ta Yi Bincike Kan Hakar Ma’adanai Da Kalubalen Tsaro A Arewa

Next Post

Kungiyar Masu Masana’antu Ta Nemi Gwamnati Ta Daidaita Harajin Da Ake Kakaba Musu

Related

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

11 hours ago
Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
Tattalin Arziki

Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island

1 week ago
Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata

2 weeks ago
Yadda Cazar Kudade Da Yawa Ke Haifar Da Raguwar Fitar Da Kaya A Tashoshin Jiragen Ruwa – NPA
Tattalin Arziki

Hukumar NPA Ta Ce Za A Kammala Aikin NSWP A Zango Na Daya A 2026

1 month ago
Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar
Tattalin Arziki

Shugaban NPA Dantsoho Ya Bayyana Aniyar Inganta Ayyukan Hukumar A Wannan Shekarar

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Nijeriya Ke Ci Gaba Da Rike Kambun Kasa Na Mafi Yawan Samar Da Danyen Mai A Afirka — OPEC

1 month ago
Next Post
Cire Tallafin Mai: Za A Fara Bai Wa Talakawa Dubu 8 Duk Wata

Kungiyar Masu Masana’antu Ta Nemi Gwamnati Ta Daidaita Harajin Da Ake Kakaba Musu

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.