ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tasirin Mata A Harkar Hakar Ma’adanai Na Kara Bayyana

by Bello Hamza
3 years ago
Mata

A ci gaba da kokarin ganin ba a bar su a baya ba, wasu gungun mata a karkashin inuwar kungiyar ‘Women in Mining in Nigeria (WIMIN)’ sun kafa reshe na 27 a yankin Babban Birnin Tarayya Abuja don shiga a dama da su a harkar hakar ma’adanai a fadin kasar nan.

A bikin kaddamar da shugabanin reshen na Abuja da aka yi a karshen mako, Shugabar kungiyar ta kasa, Dakta Janet Adeyemi, ta ranstar da kwamitin riko wanda Dakta Comfort Asokoro-Ogaji, za ta jagoranta kafin a kai ga zaban shugabanin kungiyar na dindindin.

  • Kungiyar Kasar Sin Ta Lashe Dukkan Lambobin Zinare Na Wasannin Nutso A Gasar Wasannin Kasashen Asiya
  • Barazanar Tsaro: Gwamna Kefas Ya Nemi A Tura Masa Bataliya Zuwa Taraba

A jawabinta a wajen taron, Shugabar kungiyar na kasa, Hon Adeyemi, wadda mai ilimin ma’adanai ne kuma tsohuwar ‘yar majalisar kasa ce, ta bayyana cewa, ta kafa kungiyar ce bayan da ta lura da yadda ake cutar da mata a harkar ma’adanai a Nijeriya, musamman a wuraren hakar ma’adanai na Jos da saurar sassan kasar nan, kuma ana nisantar da su daga shiga cikin harkokin kasuwancin ma’adanai a kasar nan, haka kuma ta fahimci cewa, kwararrun mata masu ilimin hakar ma’adanai na fuskantar wariya ana kuma kange su daga rike mukamai a cibiyoyi da hukumomin gudanar da harkokin ma’adanai na kasa, a kan haka ta kudiri aniyar dawo da martabar mata a harkar hakar ma’adanai a Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Ta kara da cewa, da farko, ta fuskanci turjiya daga maza amma ganin yadda ta dake da aiwatar da kudurinta, a halin yanzu an samu mata da dama da ke aiki a bangaren ma’adanai har an kai ga kafa reshen kungiyar a jihohi 27 cikin jihohi 36 da yankin babbar birnin tarayya, akwai kuma reshen kungiyar a kasashen Afirika da wasu sassan duniya har guda 96.

Ta kuma kara da cewa, in har mata suka hada kai a tsakaninsu, maza ba za su iya zarce su ba, musamman ganin harkar ma’adanai na da bangarori daban-daban da kowa zai iya samun nashi alharin ba tare da takurawa wai ba, tun daga masu haka, sarrfawa da saye da sayarwa da kuma fitarwa kasashen waje.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

A nata jawabin, shugabar kungiyar na yankin Abuja, Dakta Comfort Asokoro-Ogaji, ta ce, za ta tabbatar da amfani da matsayinta wajen bunkasa shigar mata a harkar hakar ma’adanai a yankin Abuja.

A tattaunawar da ta yi da manema labarai, ta ce, Allah ya albarkaci yankin Abuja da ma’adanai masu muhimmanci wadanda suka hada da ‘Gold, Cassiterite, Dolomite, Lead/zinc, Marble da Tantalite’.

Ta yaba wa hukumar yankin babbar birnin Abuja a kan yadda ta kirkiro da sashin na musamman don kula da harkokin ma’adanai wanda hakan zai taimaka a gaggauta samar da aikin yi da arziki ga al’umma.

Dakta Asokoro-Ogaji ta kara da cewa, “A mastayin mu na mata za mu bayar da namu gudummawar wajen aiki a bangaren hakar ma’adanai tare da tabbatar da gwamnati na samun kudaden shiga daga bangaren hakar ma’adanai kamar yadda ya kamata.

“Ya kamata mata a yankjin Abuja su amfana da wadannan albarkatun kasa da Allah ya samar a yankin. Tabbas akwai abubuwan da suke bukatar kudi amma wasu abubuwan suna bukatar jajircewa ne kawai na al’umma, idan kowa ya bayar da nasa gudummawar dole a kai ga ci gaba wanda kuma hakan zai amfanar da al’umma gaba daya.

Bincike ya nuna cewa, mata na bayar da gaggrumin gudumawa a harkar hakar ma’adanai, amma ana amfani dasu ne kawai ba tare da suna cin cikakkiyar gajiyar aikin da suke yi ba. A kan haka aka nemi shugabannin al’umma sarakuna da sauran masu ruwa da tsaki da su tsayu wajen ganin dukkan al’umma na cin gajiyar ma’adanai da Allah ya horewa kasa, ta hanyar amfani da kudaden da ake samu wajen gudanar da ayyuykan ci gaba ga al’umma tare da sa ido don kare muhalli daga cutarwar ayyukan masu hakar ma’adanai.

Mata
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Jihar Kano Za Ta Amfana Matuka Da Gidauniyar Aliko Dangote – Masu Ruwa Da Tsaki
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Nuna Damuwa Kan Sake Kamun Da DSS Ta Yi Wa Boɗejo Bayan Samun Belin EFCC
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Al’ummar Arewa Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani —Alfa Musa
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Ba Mu Taba Biyan Kudin Fansa Ba Kuma Ba Za Mu Biya Ba – Kwamishinan Katsina

MASU ALAKA

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas
Tattalin Arziki

Yadda Taron Bikin Maulidi Ya Gudana A Unguwar Mile 12 A Legas

September 4, 2026
NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
Tattalin Arziki

NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba

September 4, 2026
NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja
Tattalin Arziki

NPA Ta Tabbatar Da Maido Da Manyan Kayan Aikin Hukumar Wuta Ta Neja Delta —Babbar Manaja

August 28, 2026
Next Post
Cire Tallafin Mai: Za A Fara Bai Wa Talakawa Dubu 8 Duk Wata

Kungiyar Masu Masana’antu Ta Nemi Gwamnati Ta Daidaita Harajin Da Ake Kakaba Musu

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.