ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tasirin Mata A Harkar Hakar Ma’adanai Na Kara Bayyana

by Bello Hamza
3 years ago
Mata

A ci gaba da kokarin ganin ba a bar su a baya ba, wasu gungun mata a karkashin inuwar kungiyar ‘Women in Mining in Nigeria (WIMIN)’ sun kafa reshe na 27 a yankin Babban Birnin Tarayya Abuja don shiga a dama da su a harkar hakar ma’adanai a fadin kasar nan.

A bikin kaddamar da shugabanin reshen na Abuja da aka yi a karshen mako, Shugabar kungiyar ta kasa, Dakta Janet Adeyemi, ta ranstar da kwamitin riko wanda Dakta Comfort Asokoro-Ogaji, za ta jagoranta kafin a kai ga zaban shugabanin kungiyar na dindindin.

  • Kungiyar Kasar Sin Ta Lashe Dukkan Lambobin Zinare Na Wasannin Nutso A Gasar Wasannin Kasashen Asiya
  • Barazanar Tsaro: Gwamna Kefas Ya Nemi A Tura Masa Bataliya Zuwa Taraba

A jawabinta a wajen taron, Shugabar kungiyar na kasa, Hon Adeyemi, wadda mai ilimin ma’adanai ne kuma tsohuwar ‘yar majalisar kasa ce, ta bayyana cewa, ta kafa kungiyar ce bayan da ta lura da yadda ake cutar da mata a harkar ma’adanai a Nijeriya, musamman a wuraren hakar ma’adanai na Jos da saurar sassan kasar nan, kuma ana nisantar da su daga shiga cikin harkokin kasuwancin ma’adanai a kasar nan, haka kuma ta fahimci cewa, kwararrun mata masu ilimin hakar ma’adanai na fuskantar wariya ana kuma kange su daga rike mukamai a cibiyoyi da hukumomin gudanar da harkokin ma’adanai na kasa, a kan haka ta kudiri aniyar dawo da martabar mata a harkar hakar ma’adanai a Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Ta kara da cewa, da farko, ta fuskanci turjiya daga maza amma ganin yadda ta dake da aiwatar da kudurinta, a halin yanzu an samu mata da dama da ke aiki a bangaren ma’adanai har an kai ga kafa reshen kungiyar a jihohi 27 cikin jihohi 36 da yankin babbar birnin tarayya, akwai kuma reshen kungiyar a kasashen Afirika da wasu sassan duniya har guda 96.

Ta kuma kara da cewa, in har mata suka hada kai a tsakaninsu, maza ba za su iya zarce su ba, musamman ganin harkar ma’adanai na da bangarori daban-daban da kowa zai iya samun nashi alharin ba tare da takurawa wai ba, tun daga masu haka, sarrfawa da saye da sayarwa da kuma fitarwa kasashen waje.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

A nata jawabin, shugabar kungiyar na yankin Abuja, Dakta Comfort Asokoro-Ogaji, ta ce, za ta tabbatar da amfani da matsayinta wajen bunkasa shigar mata a harkar hakar ma’adanai a yankin Abuja.

A tattaunawar da ta yi da manema labarai, ta ce, Allah ya albarkaci yankin Abuja da ma’adanai masu muhimmanci wadanda suka hada da ‘Gold, Cassiterite, Dolomite, Lead/zinc, Marble da Tantalite’.

Ta yaba wa hukumar yankin babbar birnin Abuja a kan yadda ta kirkiro da sashin na musamman don kula da harkokin ma’adanai wanda hakan zai taimaka a gaggauta samar da aikin yi da arziki ga al’umma.

Dakta Asokoro-Ogaji ta kara da cewa, “A mastayin mu na mata za mu bayar da namu gudummawar wajen aiki a bangaren hakar ma’adanai tare da tabbatar da gwamnati na samun kudaden shiga daga bangaren hakar ma’adanai kamar yadda ya kamata.

“Ya kamata mata a yankjin Abuja su amfana da wadannan albarkatun kasa da Allah ya samar a yankin. Tabbas akwai abubuwan da suke bukatar kudi amma wasu abubuwan suna bukatar jajircewa ne kawai na al’umma, idan kowa ya bayar da nasa gudummawar dole a kai ga ci gaba wanda kuma hakan zai amfanar da al’umma gaba daya.

Bincike ya nuna cewa, mata na bayar da gaggrumin gudumawa a harkar hakar ma’adanai, amma ana amfani dasu ne kawai ba tare da suna cin cikakkiyar gajiyar aikin da suke yi ba. A kan haka aka nemi shugabannin al’umma sarakuna da sauran masu ruwa da tsaki da su tsayu wajen ganin dukkan al’umma na cin gajiyar ma’adanai da Allah ya horewa kasa, ta hanyar amfani da kudaden da ake samu wajen gudanar da ayyuykan ci gaba ga al’umma tare da sa ido don kare muhalli daga cutarwar ayyukan masu hakar ma’adanai.

Mata
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Shekara 3 Da Shirin Ceto Jihar Zamfara: Jinjina Ta Musamman Ga Gwamna Dauda Lawal
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    An Yi Tir Da ‘Yan Takarar Da Suka Fice Daga APC Saboda Faduwa Zabe
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kotu Ta Yi Gwanjon Kaddarorin Sani Sha’aban Bisa Taurin Bashi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dorewar Tattalin Arzikin Duniya Ya Dogara Ne Kan Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwa Na Afrika Ta Tsakiya, Cewar Dantsoho

MASU ALAKA

Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN
Tattalin Arziki

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026
Next Post
Cire Tallafin Mai: Za A Fara Bai Wa Talakawa Dubu 8 Duk Wata

Kungiyar Masu Masana’antu Ta Nemi Gwamnati Ta Daidaita Harajin Da Ake Kakaba Musu

LABARAI MASU NASABA

Tunisiyya Ta Sallami Kocinta Bayan Shan Kashi 5-1 A Wasan Farko Na Kofin Duniya

Tunisiyya Ta Sallami Kocinta Bayan Shan Kashi 5-1 A Wasan Farko Na Kofin Duniya

June 15, 2026
Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

June 15, 2026
ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

June 15, 2026
Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

June 15, 2026
Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

June 15, 2026
Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

June 15, 2026
An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.