• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattalin Arziki Mai Alaka Da Fasahohin Zamani Na Samun Ci Gaba A Kasashen Afirka

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Tattalin Arziki Mai Alaka Da Fasahohin Zamani Na Samun Ci Gaba A Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fannin tattalin arziki mai alaka da fasahohin zamani ya shafi zaman rayuwar dukkanmu.

Duk wani lokaci da muke biyan kudi da wayar salula, ko kuma sayen kayayyaki ta kafar yanar gizo na Internet, muna samar da gudunmowa ga ci gaban wannan fanni na tattalin arzikin.

  • Maimakon Maimaita Bukatar “Samarwa Kai Kariya” Kamata Ya Yi Amurka Ta Nazarci Ainihin Dalilin Kafa Huldar Diflomasiyya Tsakanin Ta Da Sin

Yanzu haka, wannan bangaren tattalin arziki na samun ci gaba cikin matukar sauri a kasashen Afirka. Idan mun dauki bangaren kasuwanci ta kafar shafin Internet a matsayin misali.

Sin

Mutanen da suka sayi kaya ko kuma suke yin ciniki ta kafar Internet sun kai miliyan 233 a kasashen Afirka a shekarar 2019, adadin da ake sa ran ganin karuwarsa zuwa miliyan 478, zuwa shekarar 2024.

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Wannan yanayi na samun ci gaba ya burge mutanen duniya, kana wani abun da ya fi sa ni murna, shi ne yadda fasahohi na kasar Sin ke taka muhimmiyar rawa a ciki.

A kasar Kenya, mutane sun fara yin amfani da manhajar da ake kira “Mobile Wallet” wajen biya kudi a shekarar 2007.

Wannan manhajar ta sa mutane suna iya biya da karbar kudi, ta hanyar tura sakon text, ko da kuwa wayoyin salularsu ba na zamani ba ne. Sai dai, wannan fasaha ta gamu da matsala a shekarar 2012: Yadda ake samun dimbin mutane masu yin amfani da manhajar ya sa aka kasa tafiyar da ita yadda ake bukata, inda aka fara gamuwa da matsalar karbar kudi duk ranar Juma’a.

Don daidaita wannan matsala, an gayyaci wani kamfanin kasar Sin, wanda ya taimaka wajen inganta manhajar zuwa wata da ba za a sake gamuwa da matsala yayin da ake amfani da ita ba, har ma an kara wasu hidimomi na sayen tikitin jirgin sama, da na kasa a ciki. Zuwa yanzu, manhajar “Mobile Wallet” ta samu mutane masu yin amfani da ita kimanin miliyan 30 a kasar Kenya, da sauran wasu fiye da miliyan 20 a kasashen Tanzania, da Ghana, da Masar, da dai sauransu.

Hakika muna iya ganin yadda hadin gwiwar Afirka da Sin ke tabbatar da ci gaban tattalin arziki mai alaka da fasahohin zamani a kasashen Afirka, a fannoni daban daban. Misali, a fannin kasuwanci ta kafar Internet, wani dandalin kasuwanci da wani kamfanin kasar Sin ya kafa, yana taimakawa wajen samar da kayayyaki na kasashe daban daban, zuwa mutane kimanin miliyan 300 na gabashin Afirka, da samar da guraben aikin yi ga mutane fiye da dubu 10.

Kana a bangaren horaswa, kamfanonin kasar Sin sun yi hadin kai da jami’o’in kasar Afirka da Kudu, wajen kafa cibiyoyin nazarin fasahohin sadarwa na zamani.

A cewar Abdullahi Usman, darektan sashen raya kayayyakin more rayuwa na hukumar raya fasahohin sadarwa na zamani a Najeriya, yanzu a wasu birane 17 dake wasu kasashe 15 na nahiyar Afirka, akwai kamfanoni fiye da 1500 da suke kokarin hadin gwiwa da kamfanonin kasar Sin wajen shigo da fasahohi na zamani.

Yadda wadannan kamfanonin kasashen Afirka suke kokarin hadin gwiwa da kasar Sin ba zai ba mutane mamaki ba.

Kasancewar shirin raya fasahohin zamani na cikin manyan yarjeniyoyin da kasashen Afirka suka kulla tare da kasar Sin, yasa an karfafa hadin gwiwar bangarorin 2, har zuwa shekarar 2035.

Wannan shiri ya dace da manufar kasar Sin ta “koya wa mutane fasahar kamun kifi maimakon ba su kifi kawai” a fannin hadin gwiwarta da kasashen Afirka, kana zai biya bukatar kasashen Afirka ta zamanintar da fasahohi, da raya tattalin arziki.

A yanzu mun fara ganin sakamakon shirin, kana za mu ga karin nasarorin da za a samu karkashinsa a nan gaba. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Yi Saurin Samun Karuwar Hukumomin Kula Da Hakkin Mallakar Fasaha

Next Post

Abinda Yasa Na Zabi Musulmi Mataimakina – Tinubu

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

4 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

6 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

6 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

10 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

12 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

12 hours ago
Next Post
2023: Tinubu Ya Zaɓi Kashim Shettima A Matsayin Mataimaki

Abinda Yasa Na Zabi Musulmi Mataimakina - Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.