ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattalin Arziki Mai Alaka Da Fasahohin Zamani Na Samun Ci Gaba A Kasashen Afirka

by CMG Hausa
4 years ago
Sin

Fannin tattalin arziki mai alaka da fasahohin zamani ya shafi zaman rayuwar dukkanmu.

Duk wani lokaci da muke biyan kudi da wayar salula, ko kuma sayen kayayyaki ta kafar yanar gizo na Internet, muna samar da gudunmowa ga ci gaban wannan fanni na tattalin arzikin.

  • Maimakon Maimaita Bukatar “Samarwa Kai Kariya” Kamata Ya Yi Amurka Ta Nazarci Ainihin Dalilin Kafa Huldar Diflomasiyya Tsakanin Ta Da Sin

Yanzu haka, wannan bangaren tattalin arziki na samun ci gaba cikin matukar sauri a kasashen Afirka. Idan mun dauki bangaren kasuwanci ta kafar shafin Internet a matsayin misali.

ADVERTISEMENT

Sin

Mutanen da suka sayi kaya ko kuma suke yin ciniki ta kafar Internet sun kai miliyan 233 a kasashen Afirka a shekarar 2019, adadin da ake sa ran ganin karuwarsa zuwa miliyan 478, zuwa shekarar 2024.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Wannan yanayi na samun ci gaba ya burge mutanen duniya, kana wani abun da ya fi sa ni murna, shi ne yadda fasahohi na kasar Sin ke taka muhimmiyar rawa a ciki.

A kasar Kenya, mutane sun fara yin amfani da manhajar da ake kira “Mobile Wallet” wajen biya kudi a shekarar 2007.

Wannan manhajar ta sa mutane suna iya biya da karbar kudi, ta hanyar tura sakon text, ko da kuwa wayoyin salularsu ba na zamani ba ne. Sai dai, wannan fasaha ta gamu da matsala a shekarar 2012: Yadda ake samun dimbin mutane masu yin amfani da manhajar ya sa aka kasa tafiyar da ita yadda ake bukata, inda aka fara gamuwa da matsalar karbar kudi duk ranar Juma’a.

Don daidaita wannan matsala, an gayyaci wani kamfanin kasar Sin, wanda ya taimaka wajen inganta manhajar zuwa wata da ba za a sake gamuwa da matsala yayin da ake amfani da ita ba, har ma an kara wasu hidimomi na sayen tikitin jirgin sama, da na kasa a ciki. Zuwa yanzu, manhajar “Mobile Wallet” ta samu mutane masu yin amfani da ita kimanin miliyan 30 a kasar Kenya, da sauran wasu fiye da miliyan 20 a kasashen Tanzania, da Ghana, da Masar, da dai sauransu.

Hakika muna iya ganin yadda hadin gwiwar Afirka da Sin ke tabbatar da ci gaban tattalin arziki mai alaka da fasahohin zamani a kasashen Afirka, a fannoni daban daban. Misali, a fannin kasuwanci ta kafar Internet, wani dandalin kasuwanci da wani kamfanin kasar Sin ya kafa, yana taimakawa wajen samar da kayayyaki na kasashe daban daban, zuwa mutane kimanin miliyan 300 na gabashin Afirka, da samar da guraben aikin yi ga mutane fiye da dubu 10.

Kana a bangaren horaswa, kamfanonin kasar Sin sun yi hadin kai da jami’o’in kasar Afirka da Kudu, wajen kafa cibiyoyin nazarin fasahohin sadarwa na zamani.

A cewar Abdullahi Usman, darektan sashen raya kayayyakin more rayuwa na hukumar raya fasahohin sadarwa na zamani a Najeriya, yanzu a wasu birane 17 dake wasu kasashe 15 na nahiyar Afirka, akwai kamfanoni fiye da 1500 da suke kokarin hadin gwiwa da kamfanonin kasar Sin wajen shigo da fasahohi na zamani.

Yadda wadannan kamfanonin kasashen Afirka suke kokarin hadin gwiwa da kasar Sin ba zai ba mutane mamaki ba.

Kasancewar shirin raya fasahohin zamani na cikin manyan yarjeniyoyin da kasashen Afirka suka kulla tare da kasar Sin, yasa an karfafa hadin gwiwar bangarorin 2, har zuwa shekarar 2035.

Wannan shiri ya dace da manufar kasar Sin ta “koya wa mutane fasahar kamun kifi maimakon ba su kifi kawai” a fannin hadin gwiwarta da kasashen Afirka, kana zai biya bukatar kasashen Afirka ta zamanintar da fasahohi, da raya tattalin arziki.

A yanzu mun fara ganin sakamakon shirin, kana za mu ga karin nasarorin da za a samu karkashinsa a nan gaba. (Bello Wang)

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
2023: Tinubu Ya Zaɓi Kashim Shettima A Matsayin Mataimaki

Abinda Yasa Na Zabi Musulmi Mataimakina - Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.