• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattalin Arzikin Nijeriya Na Fuskantar Koma Baya Sakamakon Zanga-zanga

by Khalid Idris Doya
11 months ago
in Labarai
0
Rana Ta 3: Duk Da Dokar Hana Fita Masu Zanga-zanga Sun Fito A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tattalin arzikin Nijeriya na fuskantar barazanar sakamakon zanga-zangar matsin rayuwa da ta barke. Yayin da kuma hukumomin tsaro suka zama cikin shiri a wasu jihohi, musamman yankin arewa maso yammacin Nijeriya. 

‘Yansanda da gwamnatoci sun ba da rahoton cewa an samu barnata kadarori, sa-tar kayan jama’a musamman a shaguna a Kaduna, Kano, Filato, da Bauchi, yayin da ‘yan daba suka kwace ragamar zanga-zangar da aka faro, lamarin da ya janyo tashin hankali.

  • Shugaba Tinubu Ya Umurci A Tabbatar Da Daƙile Masu Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba
  • Shugaban Timor-Leste Ya Yaba Kayayyaki Kirar Kasar Sin

Kazalika, an cafke masu zanga-zangar a Abuja da wasu sassan jihohin arewa dauke da tutar kasar Rasha. Sai dai hukumomin sun ce sun cafke wasu telolin da ke dinka tutar.

Ofishin jakadancin Rasha da ke Nijeriya ta fito ta ne hannunta daga lamarin, inda ta ce ba ta da masaniya kan masu daga tutar da sunan zanga-zangar matsin rayu-wa a Nijeriya.

Sai dai, shugaban sojojin Nijeriya, Janar Christopher Musa ya ce ba za su lamunci daga tutar wata kasa a cikin Nijeriya ba, ya misalta lamarin da cin amanar kasa.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

A tsawon kwanakin da aka yi ana gudanar da zanga-zangar neman kawo karshen gurbataccen shugabanci ya janyo tashin-tashina a Bauchi, Kaduna, da Filato da suka sanya dokar hana fita na awa 24 a baya-bayan nan, yayin da tun a farko ji-hohin Borno, Kano, Katsina, Jigawa, da Zamfara suka ayyana dokar hana zirga-zirga na awa 24 domin dakile tashin hankali da satar dukiyan jama’a.

Sai dai, a Jihar Bauchi a karamar hukumar Katagum ce kawai aka sanya dokar hana zirga-zirgar sabanin sauran jihoji.

Duk da cewa zuwa yanzu wasu jihohin sun sassauta dokar, amma tattalin arziki na samun koma baya a wasu sassan Nijeriya.

Kungiyar kanana da matsakaitan ‘yan kasuwa a Nijeriya (ASBON), ta ce a kalla naira biliyan 600 aka yi asara cikin kwanaki biyar.

Ita ma cibiyar ‘yan kasuwa masu zaman kansu (PPC) ta yi harsashen cewa akwai barazanar rasa naira biliyan 400 kowace rana sakamakon zanga-zangar.

Bayan rasa rayuka da aka samu an kuma samu barnata kadarori da sace kayayya-kin jama’a a shaguna, inda masu zuba jari a kamfanin musaya ta Nijeriya NEL suka rasa biliyan 92 zuwa ranar Litinin.

Rahotonni sun ce shaguna da masana’antu da gidajen mai da dama ne suka kulle sakamakon barazanar zanga-zanga.

Har ila yau, kungiyar masu sayar da man fetur ta IPMAN ta daura alhalin karancin mai da dogon layi da ake samu a ‘yan kwanakin nan kan masu zanga-zangar. Ka-kakin kungiyar IPMAN, Chinedu Ukadike shi ne ya shaida hakan.

Wani kwararren masanin tattalin arziki kuma shugaban SD & D Capital Manage-ment, Gbolade Idakolo, ya shawarci gwamnatin tarayya da ta daura damarar ma-gance bukatun masu zanga-zangar.

Ya ce ta hakan ne kawai za a samu shawo kan matsalolin da zanga-zangar ke ci gaba da haifarwa ga tattalin arziki.

Shi kuma daraktan cibiyar bunkasa harkokin ‘yan kasuwa masu zaman kansu (CPPE), Muda Yusuf, ya roki masu zanga-zangar da su janye domin kauce wa ci gaba da dagula lamarin tattalin arziki.

Ya ce, idan aka yi nazarin halin da tattalin Nijeriya ke ciki, ba bukatar kara dagula lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AsaraNijeriyaTattalin ArzikiZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Martanin ‘Yan Adawa Kan Zanga-zanga Da Jawabin Shugaban Kasa

Next Post

‘Yan Majalisar Tarayya 29 Da Suka Mutu A Kan Kujerunsu Cikin Shekara 9

Related

Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

13 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

13 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

14 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

14 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

17 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

18 hours ago
Next Post
Rufa-Rufar Cin Bashi Daga Majalisar Dokoki Ta Kasa!

‘Yan Majalisar Tarayya 29 Da Suka Mutu A Kan Kujerunsu Cikin Shekara 9

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.