ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattalin Arzikin Nijeriya Na Fuskantar Koma Baya Sakamakon Zanga-zanga

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Zanga-zanga

Tattalin arzikin Nijeriya na fuskantar barazanar sakamakon zanga-zangar matsin rayuwa da ta barke. Yayin da kuma hukumomin tsaro suka zama cikin shiri a wasu jihohi, musamman yankin arewa maso yammacin Nijeriya. 

‘Yansanda da gwamnatoci sun ba da rahoton cewa an samu barnata kadarori, sa-tar kayan jama’a musamman a shaguna a Kaduna, Kano, Filato, da Bauchi, yayin da ‘yan daba suka kwace ragamar zanga-zangar da aka faro, lamarin da ya janyo tashin hankali.

  • Shugaba Tinubu Ya Umurci A Tabbatar Da Daƙile Masu Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba
  • Shugaban Timor-Leste Ya Yaba Kayayyaki Kirar Kasar Sin

Kazalika, an cafke masu zanga-zangar a Abuja da wasu sassan jihohin arewa dauke da tutar kasar Rasha. Sai dai hukumomin sun ce sun cafke wasu telolin da ke dinka tutar.

ADVERTISEMENT

Ofishin jakadancin Rasha da ke Nijeriya ta fito ta ne hannunta daga lamarin, inda ta ce ba ta da masaniya kan masu daga tutar da sunan zanga-zangar matsin rayu-wa a Nijeriya.

Sai dai, shugaban sojojin Nijeriya, Janar Christopher Musa ya ce ba za su lamunci daga tutar wata kasa a cikin Nijeriya ba, ya misalta lamarin da cin amanar kasa.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

A tsawon kwanakin da aka yi ana gudanar da zanga-zangar neman kawo karshen gurbataccen shugabanci ya janyo tashin-tashina a Bauchi, Kaduna, da Filato da suka sanya dokar hana fita na awa 24 a baya-bayan nan, yayin da tun a farko ji-hohin Borno, Kano, Katsina, Jigawa, da Zamfara suka ayyana dokar hana zirga-zirga na awa 24 domin dakile tashin hankali da satar dukiyan jama’a.

Sai dai, a Jihar Bauchi a karamar hukumar Katagum ce kawai aka sanya dokar hana zirga-zirgar sabanin sauran jihoji.

Duk da cewa zuwa yanzu wasu jihohin sun sassauta dokar, amma tattalin arziki na samun koma baya a wasu sassan Nijeriya.

Kungiyar kanana da matsakaitan ‘yan kasuwa a Nijeriya (ASBON), ta ce a kalla naira biliyan 600 aka yi asara cikin kwanaki biyar.

Ita ma cibiyar ‘yan kasuwa masu zaman kansu (PPC) ta yi harsashen cewa akwai barazanar rasa naira biliyan 400 kowace rana sakamakon zanga-zangar.

Bayan rasa rayuka da aka samu an kuma samu barnata kadarori da sace kayayya-kin jama’a a shaguna, inda masu zuba jari a kamfanin musaya ta Nijeriya NEL suka rasa biliyan 92 zuwa ranar Litinin.

Rahotonni sun ce shaguna da masana’antu da gidajen mai da dama ne suka kulle sakamakon barazanar zanga-zanga.

Har ila yau, kungiyar masu sayar da man fetur ta IPMAN ta daura alhalin karancin mai da dogon layi da ake samu a ‘yan kwanakin nan kan masu zanga-zangar. Ka-kakin kungiyar IPMAN, Chinedu Ukadike shi ne ya shaida hakan.

Wani kwararren masanin tattalin arziki kuma shugaban SD & D Capital Manage-ment, Gbolade Idakolo, ya shawarci gwamnatin tarayya da ta daura damarar ma-gance bukatun masu zanga-zangar.

Ya ce ta hakan ne kawai za a samu shawo kan matsalolin da zanga-zangar ke ci gaba da haifarwa ga tattalin arziki.

Shi kuma daraktan cibiyar bunkasa harkokin ‘yan kasuwa masu zaman kansu (CPPE), Muda Yusuf, ya roki masu zanga-zangar da su janye domin kauce wa ci gaba da dagula lamarin tattalin arziki.

Ya ce, idan aka yi nazarin halin da tattalin Nijeriya ke ciki, ba bukatar kara dagula lamarin.

Zanga-zanga
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
Rufa-Rufar Cin Bashi Daga Majalisar Dokoki Ta Kasa!

‘Yan Majalisar Tarayya 29 Da Suka Mutu A Kan Kujerunsu Cikin Shekara 9

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.