ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattalin Arzikin Nijeriya Na Fuskantar Koma Baya Sakamakon Zanga-zanga

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Zanga-zanga

Tattalin arzikin Nijeriya na fuskantar barazanar sakamakon zanga-zangar matsin rayuwa da ta barke. Yayin da kuma hukumomin tsaro suka zama cikin shiri a wasu jihohi, musamman yankin arewa maso yammacin Nijeriya. 

‘Yansanda da gwamnatoci sun ba da rahoton cewa an samu barnata kadarori, sa-tar kayan jama’a musamman a shaguna a Kaduna, Kano, Filato, da Bauchi, yayin da ‘yan daba suka kwace ragamar zanga-zangar da aka faro, lamarin da ya janyo tashin hankali.

  • Shugaba Tinubu Ya Umurci A Tabbatar Da Daƙile Masu Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba
  • Shugaban Timor-Leste Ya Yaba Kayayyaki Kirar Kasar Sin

Kazalika, an cafke masu zanga-zangar a Abuja da wasu sassan jihohin arewa dauke da tutar kasar Rasha. Sai dai hukumomin sun ce sun cafke wasu telolin da ke dinka tutar.

ADVERTISEMENT

Ofishin jakadancin Rasha da ke Nijeriya ta fito ta ne hannunta daga lamarin, inda ta ce ba ta da masaniya kan masu daga tutar da sunan zanga-zangar matsin rayu-wa a Nijeriya.

Sai dai, shugaban sojojin Nijeriya, Janar Christopher Musa ya ce ba za su lamunci daga tutar wata kasa a cikin Nijeriya ba, ya misalta lamarin da cin amanar kasa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

A tsawon kwanakin da aka yi ana gudanar da zanga-zangar neman kawo karshen gurbataccen shugabanci ya janyo tashin-tashina a Bauchi, Kaduna, da Filato da suka sanya dokar hana fita na awa 24 a baya-bayan nan, yayin da tun a farko ji-hohin Borno, Kano, Katsina, Jigawa, da Zamfara suka ayyana dokar hana zirga-zirga na awa 24 domin dakile tashin hankali da satar dukiyan jama’a.

Sai dai, a Jihar Bauchi a karamar hukumar Katagum ce kawai aka sanya dokar hana zirga-zirgar sabanin sauran jihoji.

Duk da cewa zuwa yanzu wasu jihohin sun sassauta dokar, amma tattalin arziki na samun koma baya a wasu sassan Nijeriya.

Kungiyar kanana da matsakaitan ‘yan kasuwa a Nijeriya (ASBON), ta ce a kalla naira biliyan 600 aka yi asara cikin kwanaki biyar.

Ita ma cibiyar ‘yan kasuwa masu zaman kansu (PPC) ta yi harsashen cewa akwai barazanar rasa naira biliyan 400 kowace rana sakamakon zanga-zangar.

Bayan rasa rayuka da aka samu an kuma samu barnata kadarori da sace kayayya-kin jama’a a shaguna, inda masu zuba jari a kamfanin musaya ta Nijeriya NEL suka rasa biliyan 92 zuwa ranar Litinin.

Rahotonni sun ce shaguna da masana’antu da gidajen mai da dama ne suka kulle sakamakon barazanar zanga-zanga.

Har ila yau, kungiyar masu sayar da man fetur ta IPMAN ta daura alhalin karancin mai da dogon layi da ake samu a ‘yan kwanakin nan kan masu zanga-zangar. Ka-kakin kungiyar IPMAN, Chinedu Ukadike shi ne ya shaida hakan.

Wani kwararren masanin tattalin arziki kuma shugaban SD & D Capital Manage-ment, Gbolade Idakolo, ya shawarci gwamnatin tarayya da ta daura damarar ma-gance bukatun masu zanga-zangar.

Ya ce ta hakan ne kawai za a samu shawo kan matsalolin da zanga-zangar ke ci gaba da haifarwa ga tattalin arziki.

Shi kuma daraktan cibiyar bunkasa harkokin ‘yan kasuwa masu zaman kansu (CPPE), Muda Yusuf, ya roki masu zanga-zangar da su janye domin kauce wa ci gaba da dagula lamarin tattalin arziki.

Ya ce, idan aka yi nazarin halin da tattalin Nijeriya ke ciki, ba bukatar kara dagula lamarin.

Zanga-zanga
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Rufa-Rufar Cin Bashi Daga Majalisar Dokoki Ta Kasa!

‘Yan Majalisar Tarayya 29 Da Suka Mutu A Kan Kujerunsu Cikin Shekara 9

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.