ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattalin Arzikin Nijeriya Na Fuskantar Koma Baya Sakamakon Zanga-zanga

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Zanga-zanga

Tattalin arzikin Nijeriya na fuskantar barazanar sakamakon zanga-zangar matsin rayuwa da ta barke. Yayin da kuma hukumomin tsaro suka zama cikin shiri a wasu jihohi, musamman yankin arewa maso yammacin Nijeriya. 

‘Yansanda da gwamnatoci sun ba da rahoton cewa an samu barnata kadarori, sa-tar kayan jama’a musamman a shaguna a Kaduna, Kano, Filato, da Bauchi, yayin da ‘yan daba suka kwace ragamar zanga-zangar da aka faro, lamarin da ya janyo tashin hankali.

  • Shugaba Tinubu Ya Umurci A Tabbatar Da Daƙile Masu Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba
  • Shugaban Timor-Leste Ya Yaba Kayayyaki Kirar Kasar Sin

Kazalika, an cafke masu zanga-zangar a Abuja da wasu sassan jihohin arewa dauke da tutar kasar Rasha. Sai dai hukumomin sun ce sun cafke wasu telolin da ke dinka tutar.

ADVERTISEMENT

Ofishin jakadancin Rasha da ke Nijeriya ta fito ta ne hannunta daga lamarin, inda ta ce ba ta da masaniya kan masu daga tutar da sunan zanga-zangar matsin rayu-wa a Nijeriya.

Sai dai, shugaban sojojin Nijeriya, Janar Christopher Musa ya ce ba za su lamunci daga tutar wata kasa a cikin Nijeriya ba, ya misalta lamarin da cin amanar kasa.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

A tsawon kwanakin da aka yi ana gudanar da zanga-zangar neman kawo karshen gurbataccen shugabanci ya janyo tashin-tashina a Bauchi, Kaduna, da Filato da suka sanya dokar hana fita na awa 24 a baya-bayan nan, yayin da tun a farko ji-hohin Borno, Kano, Katsina, Jigawa, da Zamfara suka ayyana dokar hana zirga-zirga na awa 24 domin dakile tashin hankali da satar dukiyan jama’a.

Sai dai, a Jihar Bauchi a karamar hukumar Katagum ce kawai aka sanya dokar hana zirga-zirgar sabanin sauran jihoji.

Duk da cewa zuwa yanzu wasu jihohin sun sassauta dokar, amma tattalin arziki na samun koma baya a wasu sassan Nijeriya.

Kungiyar kanana da matsakaitan ‘yan kasuwa a Nijeriya (ASBON), ta ce a kalla naira biliyan 600 aka yi asara cikin kwanaki biyar.

Ita ma cibiyar ‘yan kasuwa masu zaman kansu (PPC) ta yi harsashen cewa akwai barazanar rasa naira biliyan 400 kowace rana sakamakon zanga-zangar.

Bayan rasa rayuka da aka samu an kuma samu barnata kadarori da sace kayayya-kin jama’a a shaguna, inda masu zuba jari a kamfanin musaya ta Nijeriya NEL suka rasa biliyan 92 zuwa ranar Litinin.

Rahotonni sun ce shaguna da masana’antu da gidajen mai da dama ne suka kulle sakamakon barazanar zanga-zanga.

Har ila yau, kungiyar masu sayar da man fetur ta IPMAN ta daura alhalin karancin mai da dogon layi da ake samu a ‘yan kwanakin nan kan masu zanga-zangar. Ka-kakin kungiyar IPMAN, Chinedu Ukadike shi ne ya shaida hakan.

Wani kwararren masanin tattalin arziki kuma shugaban SD & D Capital Manage-ment, Gbolade Idakolo, ya shawarci gwamnatin tarayya da ta daura damarar ma-gance bukatun masu zanga-zangar.

Ya ce ta hakan ne kawai za a samu shawo kan matsalolin da zanga-zangar ke ci gaba da haifarwa ga tattalin arziki.

Shi kuma daraktan cibiyar bunkasa harkokin ‘yan kasuwa masu zaman kansu (CPPE), Muda Yusuf, ya roki masu zanga-zangar da su janye domin kauce wa ci gaba da dagula lamarin tattalin arziki.

Ya ce, idan aka yi nazarin halin da tattalin Nijeriya ke ciki, ba bukatar kara dagula lamarin.

Zanga-zanga
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Zanga-zanga
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Zanga-zanga
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Next Post
Rufa-Rufar Cin Bashi Daga Majalisar Dokoki Ta Kasa!

‘Yan Majalisar Tarayya 29 Da Suka Mutu A Kan Kujerunsu Cikin Shekara 9

LABARAI MASU NASABA

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Zanga-zanga

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Zanga-zanga

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.