• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Bunkasa Daga Dukkanin Fannoni Duk Da Sauye-sauye Da Ake Fuskanta

bySulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
Sin

Tun a rabin farkon shekarar nan ta 2024, tattalin arzikin kasar Sin ya bunkasa da kaso 5 bisa dari, wanda hakan ke nuni ga farfadowarsa bisa daidaito, duk kuwa da kalubalen da yake fuskanta a gida da ketare. Masharhanta da dama na ganin hakan shaida ce dake tabbatar da matsayin tattalin arzikin kasar Sin na kasancewa injin dake ingiza ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya.

Ko shakka babu ana iya ganin sassa da suka haifar da wannan ci gaba. Musamman fannin fadadar cinikayya, wadda cikin rubu’in farko na bana ta bunkasa da kaso 6.1 bisa dari, sannan akwai fannin karuwar yawan hatsi da kasar ta samu a kakar bana. Ga kuma fannin sarrafa hajoji daga masana’antu ba tare da gurbata muhalli ba, da na bayar da hidimomi, da fannin kere-keren injuna masu sarrafa kansu, da fannin samar da sabbin makamashi, wadanda dukkanin suke karfafa bunkasar tattalin arzikin kasar ta Sin.

  • Shugaban Amurka, Joe Biden Ya Kamu Da Cutar Covid-19
  • Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Dukkanin Sassa Da Nufin Daga Martabar BRI Zuwa Babban Matsayi

A daya hannun kuma, ana iya ganin yadda bukatun sayayya a cikin gida ke karuwa, yayin da bukatun hajoji daga ketare ma ke habaka, har ma wasu alkaluma suka nuna karuwar hajoji da hidimomin da kasar Sin ke samarwa ga ketare, sun samar da karin kaso 13.9 bisa dari na ci gaban tattalin arzikin kasar a rabin farko na shekarar nan.

A fannin samar da manufofi ma, gwamnatin Sin ta taka rawar gani wajen aiwatar da manufofi daban daban, wadanda ke ingiza ci gaba, da karfafa sayayya da kare sana’o’i.

A kan ce, “Juma’ar da za ta yi kyau tun daga Laraba ake gane ta”. Tun daga rabin farko na shekarar bana, an ga ci gaba a fannonin bunkasar tattalin arzikin Sin bisa daidaito da karsashi, don haka ko shakka babu wannan ci gaba zai dore, karkashin karfin sashen sarrafa kayayyaki da bayar da hidimomi, da kyakkyawan yanayin zamantakewar al’umma. A daya bangaren kuma, kwazon da ake yi a fannin zurfafa gyare-gyare a dukkanin fannoni zai ci gaba da karfafa tushe, da samar da tabbaci ga cimma zamanintarwa irin ta kasar Sin. (Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
Zanga-zangar Tsadar Rayuwa: Ina Mafita?

Zanga-zangar Tsadar Rayuwa: Ina Mafita?

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version