• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Bunkasa Daga Dukkanin Fannoni Duk Da Sauye-sauye Da Ake Fuskanta

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
Sin

Tun a rabin farkon shekarar nan ta 2024, tattalin arzikin kasar Sin ya bunkasa da kaso 5 bisa dari, wanda hakan ke nuni ga farfadowarsa bisa daidaito, duk kuwa da kalubalen da yake fuskanta a gida da ketare. Masharhanta da dama na ganin hakan shaida ce dake tabbatar da matsayin tattalin arzikin kasar Sin na kasancewa injin dake ingiza ci gaban tattalin arzikin duniya baki daya.

Ko shakka babu ana iya ganin sassa da suka haifar da wannan ci gaba. Musamman fannin fadadar cinikayya, wadda cikin rubu’in farko na bana ta bunkasa da kaso 6.1 bisa dari, sannan akwai fannin karuwar yawan hatsi da kasar ta samu a kakar bana. Ga kuma fannin sarrafa hajoji daga masana’antu ba tare da gurbata muhalli ba, da na bayar da hidimomi, da fannin kere-keren injuna masu sarrafa kansu, da fannin samar da sabbin makamashi, wadanda dukkanin suke karfafa bunkasar tattalin arzikin kasar ta Sin.

  • Shugaban Amurka, Joe Biden Ya Kamu Da Cutar Covid-19
  • Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da Dukkanin Sassa Da Nufin Daga Martabar BRI Zuwa Babban Matsayi

A daya hannun kuma, ana iya ganin yadda bukatun sayayya a cikin gida ke karuwa, yayin da bukatun hajoji daga ketare ma ke habaka, har ma wasu alkaluma suka nuna karuwar hajoji da hidimomin da kasar Sin ke samarwa ga ketare, sun samar da karin kaso 13.9 bisa dari na ci gaban tattalin arzikin kasar a rabin farko na shekarar nan.

A fannin samar da manufofi ma, gwamnatin Sin ta taka rawar gani wajen aiwatar da manufofi daban daban, wadanda ke ingiza ci gaba, da karfafa sayayya da kare sana’o’i.

A kan ce, “Juma’ar da za ta yi kyau tun daga Laraba ake gane ta”. Tun daga rabin farko na shekarar bana, an ga ci gaba a fannonin bunkasar tattalin arzikin Sin bisa daidaito da karsashi, don haka ko shakka babu wannan ci gaba zai dore, karkashin karfin sashen sarrafa kayayyaki da bayar da hidimomi, da kyakkyawan yanayin zamantakewar al’umma. A daya bangaren kuma, kwazon da ake yi a fannin zurfafa gyare-gyare a dukkanin fannoni zai ci gaba da karfafa tushe, da samar da tabbaci ga cimma zamanintarwa irin ta kasar Sin. (Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka
Daga Birnin Sin

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
Next Post
Zanga-zangar Tsadar Rayuwa: Ina Mafita?

Zanga-zangar Tsadar Rayuwa: Ina Mafita?

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.