• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

by Sulaiman
3 days ago
in Labarai
0
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata tawaga daga Gwamnatin Tarayya ta halarci jana’izar fitaccen ɗan kasuwa kuma dattijon Arewa, Alhaji Aminu Ɗantata, wadda aka yi a birnin Madina na ƙasar Saudiyya a ranar Talata.

Alhaji Ɗantata ya rasu ne a ranar Asabar a birnin Abu Dhabi, a kasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE), yana da shekara 94 a duniya. Bisa ga wasiyyar sa ne aka binne shi a Madina.

  • Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma
  • An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

Ɗan sa, Alhaji Tajudeen Ɗantata, da Alhaji Aliko Ɗangote, sun isa Madina a safiyar Talata tare da gawar marigayin, suna tare da wasu ‘yan’uwa na kusa.

Tawagar ta Gwamnatin Tarayya ta bar Nijeriya ne a daren Lahadi, inda suka isa Madina da sanyin safiyar Litinin.

Ministan Tsaro kuma tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Muhammad Badaru Abubakar, shi ne ya jagoranci tawagar.

Labarai Masu Nasaba

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Dantata

Cikin tawagar akwai Ministan Shari’a kuma Antoni Janar na Ƙasa, Yarima Lateef Fagbemi, SAN; a Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris; da Ƙaramin Ministan Harkokin Gidaje da Cigaban Birane, Hon. Yusuf Abdullahi Ata; da kuma Hassan Abdullahi, Daraktan Tsaro na Cikin Gida a ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (NSA), wanda ya wakilci NSA.

Wasu fitattun malamai na addinin Musulunci da suka kasance cikin tawagar sun haɗa da Dakta Bashir Aliyu Umar, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, da Limamin Masallacin Ɗantata da ke Abuja, Khalifa Abdullahi Muhammad.

Jami’an Ofishin Jakadancin Nijeriya da ke Jiddah sun haɗu da tawagar, ƙarƙashin jagorancin Ambasada Ibrahim Modibbo, tare da Ambasada Mu’azzam Ibrahim Nayaya, da Manjo Janar Adamu Hassan, waɗanda suka jagoranci shirye-shiryen jana’izar.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, da tsohon Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dakta Abdullahi Ganduje, su ma sun halarci jana’izar tare da Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, da na Jigawa, Alhaji Umar Namadi.

Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II da Sarki Aminu Ado Bayero su ma sun halarci jana’izar.

An binne Alhaji Aminu Ɗantata a maƙabartar Baƙiyya da ke Madina bayan an gudanar da sallar jana’iza da yammaci a Masallacin Manzon Allah (SAW).


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

Next Post

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

Related

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet
Labarai

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

7 hours ago
Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
Ra'ayi Riga

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

11 hours ago
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa
Labarai

Abba Ya Yi Sabbin Naɗe-naɗe A Jihar Kano

12 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

12 hours ago
Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari
Labarai

Haɗarin Da Ke Ƙunshe Da Jin Ɓangare Ɗaya Na Labari

13 hours ago
NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya
Labarai

NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya

14 hours ago
Next Post
An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba

July 4, 2025
Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

Sin Za Ta Gaggauta Aikin Raya Sana’o’in Samar Da Wutar Lantarki Daga Zafin Rana

July 4, 2025
Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

Ku Zama Cikin Shirin Samun Sauyin Yanayi – NiMet

July 4, 2025
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

July 4, 2025
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

July 4, 2025
Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin

July 4, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

July 4, 2025
Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu

July 4, 2025
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

July 4, 2025
Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba

July 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.