Tawagar likitocin kasar Sin ta 24 wadda ke jamhuriyar Nijer, ta ba da horon fasahar likitancin gargajiya ta Sin a babban asibitin Nijar dake birnin Yamai, wanda ya jawo hankulan mahalarta kusan 50, ciki har da manyan ma’aikatan kiwon lafiya na asibitin, da dalibai daga kwalejin likitanci ta jami’ar Yamai da kuma masu sha’awar likitancin gargajiya na Sin.
Zheng Zhida, shugaban tawagar likitoci ta Sin, ya bayyana a bikin kaddamar da horon cewa, tun bayan kafa cibiyar likitancin gargajiya na Sin dake babban asibitin Nijar, duban-dubatar marasa lafiya sun amfana da ita. Ya ce horon na wannan karo ba darasi ne kawai dake bada fasahohin likitanci ba, wani aiki ne na mu’ammalar al’adu.
A nasa bangare, farfesa Mamane Daou, daraktan babban asibitin Nijar, ya bayyana cewa, wannan horon ya ba da dama mai daraja ga ma’aikatan ba da jinya na asibitin wajen samun zurfin fahimtar likitancin gargajiya na Sin da kuma koyon dabaru masu amfani. Ya ce cikin ‘yan shekarun nan, likitancin gargajiya na Sin ya taimaka sosai ga yawancin marasa lafiya na Nijar bisa fa’idodin da yake da su na sauki da aminci da karancin farashi. A nan gaba, ana fatan karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu don sa kaimi ga kara amfani da fasahar likitancin gargajiya na Sin a Nijar. (Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp