• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Masoyin Arewa Ne Ba Kamar Yadda Wasu Ke Juya Maganar Ba – Shettima

by El-Zaharadeen Umar
1 year ago
in Labarai
0
Tinubu Masoyin Arewa Ne Ba Kamar Yadda Wasu Ke Juya Maganar Ba – Shettima
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Mataimakin Shugaban Kasa Sanata Kashim Shettima ya bayyana cewa shugaban Kasa Bola Ahmad Tunibu Masoyin Arewa da ‘yan arewa ne , ba kamar yadda wasu ke juya zance da cewa shi makiyin arewa ne ba.
Sanata Kashin Shettima ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi makoncin wasu ‘yan jaridu na arewacin Nijeriya a ofishinsa  da ke  fadar Shugaban Kasa, a Abuja.
  • Zanga-zanga: Gwamnatin Kano Ba za Ta Amince Da Barnata Dukiyar Al’umma Ba
  • Zaben Kananan Hukumomi: Za A Yi Wa ‘Yan Takara Gwajin Kwaya A Kano
Ya kuma  bayyana cewa babu abin da gwamnatin suke buƙata a halin yanzu kamar goyon baya domin su samu damar shimfida ayyukan alheri ga al’ummar Nijeriya.
“Maganar cewa shugaba Bola Tinubu ba ya san mutanen arewa ko addinin Musulmi ba gaskiya ba ne, idan aka duba irin muƙaman da ya ba da a gwamantinsa musamman a manyan ma’aikatu da hukumomin gwamnati.” In ji shi.
Sanata Kashim Shattima ya yi ƙarin haske game da zanga-zangar da wasu matasa suke shirin yi, inda ya bayyana cewa dokar ƙasa ta ba su dama, sai dai ya ce babu wani abu a cikinta da ya wuce koma baya.
A cewarsa, akwai bukatar kafafen yaɗa labarai a wannan lokaci su sanar da al’umma cewa yin zanga-zanga a kan tituna ba zai kawo ci gaba a arewa ba.
“Yau ɗin nan, idan aka ce za a yi wannan zanga-zanga Allah kaɗai ya san irin asarar da za a tafka, duk da cewa ‘yan ƙasa suna da hakkin yin ta, amma matsala wasu marasa kishi na iya canza mata manufa” in ji Shettima.
Ya ƙara da cewa , alƙaluma sun nuna irin yadda shugaban ƙasa ya raba muƙamai a hukumomin ƙasar nan, musamman muhimman wurare da suka haɗa ma’aikatar gona da tsaro da harkar sadarwa da kiwon lafiya da sauransu.
Mataimakin shugaban kasar ya ce wannan gwamnati tana da kyakkyawar tanadi da ta yi wa ‘yan ƙasa domin inganta rayuwar mutanen arewa ta hanyar ɓullo da wasu tsare-tsare don tunkarar matsalar da yankin yake fuskanta.
Sanata Kashin Shettima ya ba da misalin da  ƙirƙirar sabuwar ma’aikatar bunƙasa noma da kiwo, haka na nuna irin yadda shugaba Tunibu ke kaunar arewa, amma wasu na juya labarin da cewa Tunibu makiyin arewa ne.
Kamar yadda Sanata Kashin Shettima ya jefa tambaya inda ya ce wane ne ya sanya hannu a kan dokar hukumar farfaɗo da yankin arewa maso yamma? Kuma wane ne ya kirkiri ma’aikatar bunƙasa noma da kiwo?
Ya ce wannan shugaban ne dai ya amince da a ƙaddamar da tsarin yin amfani da matakin soja da kuma na diplomasiya domin tunkarar matsalar tsaro a arewa maso yamma da zai taimaka wajen warware ta.
Ya ƙara da cewa ta hanyar ɓullo da sabon shirin ECOSYSTEM ga waɗanda iftila’in hare-haren ‘yan bindiga ya shafa, wannan shirin zai inganta rayuwar ‘yan arewa.
Sanata Kashin Shettima ya roki ‘yan jaridu da su haɗa kai su zama tsintsiya maɗaurinki ɗaya wajen samar da ci gaba a arewacin Nijeriya, ya ce wannan gwamnati tana buƙatar addu’o’i a irin wannan lokaci domin samun nasara, amma yanzu ba lokacin zanga-zanga ba ne.
“Mu a nan arewa muna buƙatar  bunƙasa ayyukan ci gaba waɗanda suke da mahimmancin a Nijeriya, saboda haka ba zamu kyale abubuwa su lalace ba” inji shi
Kazalika Sanata Kashin Shettima ya yi kira ga ‘yan jaridu na arewacin Nijeriya da su faɗakar da al’umma irin manyan muƙaman da shugaba Tunibu ya bai wa ‘yan arewa a gwamantinsa domin a bunƙasa ta.
Daga ƙarshe mataimakin shugaban ƙasan ya yi kira ga ‘yan arewa da su goyi bayan gwamnati mai ci yanzu domin a samu cigaba mai ɗorawa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaKashim ShettimaTinubuZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Taron FOCAC Zai Taimaki Kasashen Afirka Wajen Cimma Burinsu Na Raya Kasa

Next Post

Kasurgumin Dan Ta’adda Ya Mika Wuya Ga Sojoji A Borno

Related

Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

8 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

9 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

10 hours ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

11 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

13 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

14 hours ago
Next Post
Sojoji

Kasurgumin Dan Ta'adda Ya Mika Wuya Ga Sojoji A Borno

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.