ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Masoyin Arewa Ne Ba Kamar Yadda Wasu Ke Juya Maganar Ba – Shettima

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
Arewa

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

Mataimakin Shugaban Kasa Sanata Kashim Shettima ya bayyana cewa shugaban Kasa Bola Ahmad Tunibu Masoyin Arewa da ‘yan arewa ne , ba kamar yadda wasu ke juya zance da cewa shi makiyin arewa ne ba.
Sanata Kashin Shettima ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi makoncin wasu ‘yan jaridu na arewacin Nijeriya a ofishinsa  da ke  fadar Shugaban Kasa, a Abuja.
  • Zanga-zanga: Gwamnatin Kano Ba za Ta Amince Da Barnata Dukiyar Al’umma Ba
  • Zaben Kananan Hukumomi: Za A Yi Wa ‘Yan Takara Gwajin Kwaya A Kano
Ya kuma  bayyana cewa babu abin da gwamnatin suke buƙata a halin yanzu kamar goyon baya domin su samu damar shimfida ayyukan alheri ga al’ummar Nijeriya.
“Maganar cewa shugaba Bola Tinubu ba ya san mutanen arewa ko addinin Musulmi ba gaskiya ba ne, idan aka duba irin muƙaman da ya ba da a gwamantinsa musamman a manyan ma’aikatu da hukumomin gwamnati.” In ji shi.
Sanata Kashim Shattima ya yi ƙarin haske game da zanga-zangar da wasu matasa suke shirin yi, inda ya bayyana cewa dokar ƙasa ta ba su dama, sai dai ya ce babu wani abu a cikinta da ya wuce koma baya.
A cewarsa, akwai bukatar kafafen yaɗa labarai a wannan lokaci su sanar da al’umma cewa yin zanga-zanga a kan tituna ba zai kawo ci gaba a arewa ba.
“Yau ɗin nan, idan aka ce za a yi wannan zanga-zanga Allah kaɗai ya san irin asarar da za a tafka, duk da cewa ‘yan ƙasa suna da hakkin yin ta, amma matsala wasu marasa kishi na iya canza mata manufa” in ji Shettima.
Ya ƙara da cewa , alƙaluma sun nuna irin yadda shugaban ƙasa ya raba muƙamai a hukumomin ƙasar nan, musamman muhimman wurare da suka haɗa ma’aikatar gona da tsaro da harkar sadarwa da kiwon lafiya da sauransu.
Mataimakin shugaban kasar ya ce wannan gwamnati tana da kyakkyawar tanadi da ta yi wa ‘yan ƙasa domin inganta rayuwar mutanen arewa ta hanyar ɓullo da wasu tsare-tsare don tunkarar matsalar da yankin yake fuskanta.
Sanata Kashin Shettima ya ba da misalin da  ƙirƙirar sabuwar ma’aikatar bunƙasa noma da kiwo, haka na nuna irin yadda shugaba Tunibu ke kaunar arewa, amma wasu na juya labarin da cewa Tunibu makiyin arewa ne.
Kamar yadda Sanata Kashin Shettima ya jefa tambaya inda ya ce wane ne ya sanya hannu a kan dokar hukumar farfaɗo da yankin arewa maso yamma? Kuma wane ne ya kirkiri ma’aikatar bunƙasa noma da kiwo?
Ya ce wannan shugaban ne dai ya amince da a ƙaddamar da tsarin yin amfani da matakin soja da kuma na diplomasiya domin tunkarar matsalar tsaro a arewa maso yamma da zai taimaka wajen warware ta.
Ya ƙara da cewa ta hanyar ɓullo da sabon shirin ECOSYSTEM ga waɗanda iftila’in hare-haren ‘yan bindiga ya shafa, wannan shirin zai inganta rayuwar ‘yan arewa.
Sanata Kashin Shettima ya roki ‘yan jaridu da su haɗa kai su zama tsintsiya maɗaurinki ɗaya wajen samar da ci gaba a arewacin Nijeriya, ya ce wannan gwamnati tana buƙatar addu’o’i a irin wannan lokaci domin samun nasara, amma yanzu ba lokacin zanga-zanga ba ne.
“Mu a nan arewa muna buƙatar  bunƙasa ayyukan ci gaba waɗanda suke da mahimmancin a Nijeriya, saboda haka ba zamu kyale abubuwa su lalace ba” inji shi
Kazalika Sanata Kashin Shettima ya yi kira ga ‘yan jaridu na arewacin Nijeriya da su faɗakar da al’umma irin manyan muƙaman da shugaba Tunibu ya bai wa ‘yan arewa a gwamantinsa domin a bunƙasa ta.
Daga ƙarshe mataimakin shugaban ƙasan ya yi kira ga ‘yan arewa da su goyi bayan gwamnati mai ci yanzu domin a samu cigaba mai ɗorawa.
Arewa
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Next Post
Sojoji

Kasurgumin Dan Ta'adda Ya Mika Wuya Ga Sojoji A Borno

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.