• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ne Mafi Cancantar Magance Matsalolin Nijeriya, In Ji Bakin- Zuwo

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
in Siyasa
0
Tinubu Ne Mafi Cancantar Magance Matsalolin Nijeriya, In Ji Bakin- Zuwo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kungiyar fafutukar neman zaben Bola Ahmad Tinubu (Tinubu Support Organisation) a Jihar Kano, Alhaji Yusuf Yunusa Bakin- Zuwo ya bayyana cewar dan takarar na jam’iyyar APC ne mafi cancanta da dacewar Shugabancin Nijeriya a 2023.

A cewarsa tsohon Gwamnan na Jihar Lagas nagartaccen dan siyasa ne wanda ke da kwarewa da gogewar shugabanci, sanin ciki da wajen matsalolin al’umma, lakantar hanyoyin magance su da sanin makamar iya hada kan kasa da fahimtar juna a tsakanin addinai.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Sanda A Harin Da Suka Kai Ofishin INEC A Enugu

 

Bakin- Zuwo wanda kuma fitaccen dan kasuwar Kasa da Kasa ne ya bayyana hakan ne a tattaunawarsa da manema labarai a Sakkwato a rangadin tallata takarar Tinubu yana cewar a kungiyar TSO a karkashin jagorancin Shugabanta na Kasa (DG) Hon. Aminu Sulaiman su kan shiga lungu da sakon Kasar nan domin yada kyawawan manufofi da kudurorin Tinubu ga al’ummar Kasar nan sama da kowace kungiya.

Ya ce “Nijeriya na bukatar hazikin gwarzon shugaba mai gaskiya da adalci wanda zai bunkasa tattalin arziki, inganta haraji, habaka kasuwanci, fitowa da hanyoyin rage dogaro da man fetur, karawa Jihohi kason wata- wata na Gwamnatin Tarayya da uwa uba kammala hobbasar kwazon Shugaba Buhari wajen kawar da matsalolin tsaro da yaki da ta’addanci.”

Labarai Masu Nasaba

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

Ya kara da cewar “Gagarumar karbuwar da Jagaban ya samu daga Arewaci da Kudancin Kasar nan babbar alama ce ta samun nasararsa ta zama Magajin Shugaba Buhari ta hanyar yi wa jam’iyyun adawa bugun ‘ya’yan kadanya wanda muna da tabbacin a budadden mulkinsa za a samu yadda da aminci a tsakanin Gwamnati da wadanda ake mulki.”

“Idan a na maganar karbuwa Tinubu a Nijeriya, Kano ba a ma maganarta domin 100 bisa 100 Kanawa za su zazzaga masa ruwan kuri’u kuma kowa ya san tasiri da girman kuri’un Kano a siyasar Nijeriya, hatta nan Sakkwato da take Jihar PDP, kuma Jihar shugaban yekuwar neman zaben PDP, za mu ba Atiku da Tambuwal mamaki in sha Allah.” In ji shi.

A cewar Bakin- Zuwo, Tinubu jagora ne nagari mai kima da tasiri, mai fada da cikawa wanda a kodayaushe ci- gaba da bunkasar al’umma shine burinsa don haka zabensa a matsayin Shugaban Kasa zabe ne na gina kasa, inganta jin dadi da walwalar jama’a, yaki da fatara, bunkasa noma da kiyo, inganta wutar lantarki, farfado da masana’antu, bunkasa hanyoyin kirkirar sababbin abubuwa ta hanyar inganta kimiya da fasaha da shigowar masu zuba jari tare da magance matsalolin ilimi da kiyon lafiya tare da shayar da al’umma romon mulkin Dimokuradiyya a dukkanin matakai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xie Feng: Sin Ta Sha Alwashin Kara Bude Kofa Da Samar Da Damammakin Zurfafa Hadin Gwiwar Cimma Moriyar Juna

Next Post

DSS Ta Mamaye CBN, Ta Kwace Ragamar Ofishin Emefiele

Related

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago
Siyasa

Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago

4 days ago
Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)
Siyasa

Tarihin Ƴan Majalisar Farko Kafin Da Kuma Zamanin Mulkin Mallaka (3)

4 days ago
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC
Siyasa

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

5 days ago
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya
Siyasa

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

6 days ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

1 week ago
APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami
Manyan Labarai

APC Ce Ke Kai Mana Hari Saboda Siyasa – Malami

1 week ago
Next Post
DSS Ta Mamaye CBN, Ta Kwace Ragamar Ofishin Emefiele

DSS Ta Mamaye CBN, Ta Kwace Ragamar Ofishin Emefiele

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.