• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ne Mafi Cancantar Magance Matsalolin Nijeriya, In Ji Bakin- Zuwo

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
in Siyasa
0
Tinubu Ne Mafi Cancantar Magance Matsalolin Nijeriya, In Ji Bakin- Zuwo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kungiyar fafutukar neman zaben Bola Ahmad Tinubu (Tinubu Support Organisation) a Jihar Kano, Alhaji Yusuf Yunusa Bakin- Zuwo ya bayyana cewar dan takarar na jam’iyyar APC ne mafi cancanta da dacewar Shugabancin Nijeriya a 2023.

A cewarsa tsohon Gwamnan na Jihar Lagas nagartaccen dan siyasa ne wanda ke da kwarewa da gogewar shugabanci, sanin ciki da wajen matsalolin al’umma, lakantar hanyoyin magance su da sanin makamar iya hada kan kasa da fahimtar juna a tsakanin addinai.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Sanda A Harin Da Suka Kai Ofishin INEC A Enugu

 

Bakin- Zuwo wanda kuma fitaccen dan kasuwar Kasa da Kasa ne ya bayyana hakan ne a tattaunawarsa da manema labarai a Sakkwato a rangadin tallata takarar Tinubu yana cewar a kungiyar TSO a karkashin jagorancin Shugabanta na Kasa (DG) Hon. Aminu Sulaiman su kan shiga lungu da sakon Kasar nan domin yada kyawawan manufofi da kudurorin Tinubu ga al’ummar Kasar nan sama da kowace kungiya.

Ya ce “Nijeriya na bukatar hazikin gwarzon shugaba mai gaskiya da adalci wanda zai bunkasa tattalin arziki, inganta haraji, habaka kasuwanci, fitowa da hanyoyin rage dogaro da man fetur, karawa Jihohi kason wata- wata na Gwamnatin Tarayya da uwa uba kammala hobbasar kwazon Shugaba Buhari wajen kawar da matsalolin tsaro da yaki da ta’addanci.”

Labarai Masu Nasaba

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

Ya kara da cewar “Gagarumar karbuwar da Jagaban ya samu daga Arewaci da Kudancin Kasar nan babbar alama ce ta samun nasararsa ta zama Magajin Shugaba Buhari ta hanyar yi wa jam’iyyun adawa bugun ‘ya’yan kadanya wanda muna da tabbacin a budadden mulkinsa za a samu yadda da aminci a tsakanin Gwamnati da wadanda ake mulki.”

“Idan a na maganar karbuwa Tinubu a Nijeriya, Kano ba a ma maganarta domin 100 bisa 100 Kanawa za su zazzaga masa ruwan kuri’u kuma kowa ya san tasiri da girman kuri’un Kano a siyasar Nijeriya, hatta nan Sakkwato da take Jihar PDP, kuma Jihar shugaban yekuwar neman zaben PDP, za mu ba Atiku da Tambuwal mamaki in sha Allah.” In ji shi.

A cewar Bakin- Zuwo, Tinubu jagora ne nagari mai kima da tasiri, mai fada da cikawa wanda a kodayaushe ci- gaba da bunkasar al’umma shine burinsa don haka zabensa a matsayin Shugaban Kasa zabe ne na gina kasa, inganta jin dadi da walwalar jama’a, yaki da fatara, bunkasa noma da kiyo, inganta wutar lantarki, farfado da masana’antu, bunkasa hanyoyin kirkirar sababbin abubuwa ta hanyar inganta kimiya da fasaha da shigowar masu zuba jari tare da magance matsalolin ilimi da kiyon lafiya tare da shayar da al’umma romon mulkin Dimokuradiyya a dukkanin matakai.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Xie Feng: Sin Ta Sha Alwashin Kara Bude Kofa Da Samar Da Damammakin Zurfafa Hadin Gwiwar Cimma Moriyar Juna

Next Post

DSS Ta Mamaye CBN, Ta Kwace Ragamar Ofishin Emefiele

Related

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12
Siyasa

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

1 hour ago
Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa
Siyasa

Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

10 hours ago
2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa
Siyasa

2027: APC Da ADC Na Gwagwarmayar Neman Samun Goyon Bayan Mutanen Arewa

1 day ago
Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili
Siyasa

Majalisar Dokokin Sokoto Ta Aike Wa  Kwamishina Sammaci, Duba Dalili

1 day ago
Tinubu Ya Cika AlÆ™awurran Da Ya ÆŠauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa
Siyasa

Tinubu Ya Cika AlÆ™awurran Da Ya ÆŠauka – Ƙungiyar Gwamnonin Arewa

2 days ago
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Labarai

2027: Ba Mu Kafa HaÉ—akarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC

3 days ago
Next Post
DSS Ta Mamaye CBN, Ta Kwace Ragamar Ofishin Emefiele

DSS Ta Mamaye CBN, Ta Kwace Ragamar Ofishin Emefiele

LABARAI MASU NASABA

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya KarÉ“i Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya KarÉ“i Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi AlÆ™awarin Biyan BuÆ™atunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi AlÆ™awarin Biyan BuÆ™atunsu 

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.