ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ne Mafi Cancantar Magance Matsalolin Nijeriya, In Ji Bakin- Zuwo

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
tinubu

Shugaban Kungiyar fafutukar neman zaben Bola Ahmad Tinubu (Tinubu Support Organisation) a Jihar Kano, Alhaji Yusuf Yunusa Bakin- Zuwo ya bayyana cewar dan takarar na jam’iyyar APC ne mafi cancanta da dacewar Shugabancin Nijeriya a 2023.

A cewarsa tsohon Gwamnan na Jihar Lagas nagartaccen dan siyasa ne wanda ke da kwarewa da gogewar shugabanci, sanin ciki da wajen matsalolin al’umma, lakantar hanyoyin magance su da sanin makamar iya hada kan kasa da fahimtar juna a tsakanin addinai.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Sanda A Harin Da Suka Kai Ofishin INEC A Enugu

 

ADVERTISEMENT

Bakin- Zuwo wanda kuma fitaccen dan kasuwar Kasa da Kasa ne ya bayyana hakan ne a tattaunawarsa da manema labarai a Sakkwato a rangadin tallata takarar Tinubu yana cewar a kungiyar TSO a karkashin jagorancin Shugabanta na Kasa (DG) Hon. Aminu Sulaiman su kan shiga lungu da sakon Kasar nan domin yada kyawawan manufofi da kudurorin Tinubu ga al’ummar Kasar nan sama da kowace kungiya.

Ya ce “Nijeriya na bukatar hazikin gwarzon shugaba mai gaskiya da adalci wanda zai bunkasa tattalin arziki, inganta haraji, habaka kasuwanci, fitowa da hanyoyin rage dogaro da man fetur, karawa Jihohi kason wata- wata na Gwamnatin Tarayya da uwa uba kammala hobbasar kwazon Shugaba Buhari wajen kawar da matsalolin tsaro da yaki da ta’addanci.”

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

Ya kara da cewar “Gagarumar karbuwar da Jagaban ya samu daga Arewaci da Kudancin Kasar nan babbar alama ce ta samun nasararsa ta zama Magajin Shugaba Buhari ta hanyar yi wa jam’iyyun adawa bugun ‘ya’yan kadanya wanda muna da tabbacin a budadden mulkinsa za a samu yadda da aminci a tsakanin Gwamnati da wadanda ake mulki.”

“Idan a na maganar karbuwa Tinubu a Nijeriya, Kano ba a ma maganarta domin 100 bisa 100 Kanawa za su zazzaga masa ruwan kuri’u kuma kowa ya san tasiri da girman kuri’un Kano a siyasar Nijeriya, hatta nan Sakkwato da take Jihar PDP, kuma Jihar shugaban yekuwar neman zaben PDP, za mu ba Atiku da Tambuwal mamaki in sha Allah.” In ji shi.

A cewar Bakin- Zuwo, Tinubu jagora ne nagari mai kima da tasiri, mai fada da cikawa wanda a kodayaushe ci- gaba da bunkasar al’umma shine burinsa don haka zabensa a matsayin Shugaban Kasa zabe ne na gina kasa, inganta jin dadi da walwalar jama’a, yaki da fatara, bunkasa noma da kiyo, inganta wutar lantarki, farfado da masana’antu, bunkasa hanyoyin kirkirar sababbin abubuwa ta hanyar inganta kimiya da fasaha da shigowar masu zuba jari tare da magance matsalolin ilimi da kiyon lafiya tare da shayar da al’umma romon mulkin Dimokuradiyya a dukkanin matakai.

tinubu
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Shekara 200 Bayan Shehu Ɗan Fodiyo: Hubbarensa Na Ci Gaba Zama Wajen Ziyara Da Neman Tabarruki
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

MASU ALAKA

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa
Siyasa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci
Siyasa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Next Post
DSS Ta Mamaye CBN, Ta Kwace Ragamar Ofishin Emefiele

DSS Ta Mamaye CBN, Ta Kwace Ragamar Ofishin Emefiele

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.