ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ne Mafi Cancantar Magance Matsalolin Nijeriya, In Ji Bakin- Zuwo

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
4 years ago
tinubu

Shugaban Kungiyar fafutukar neman zaben Bola Ahmad Tinubu (Tinubu Support Organisation) a Jihar Kano, Alhaji Yusuf Yunusa Bakin- Zuwo ya bayyana cewar dan takarar na jam’iyyar APC ne mafi cancanta da dacewar Shugabancin Nijeriya a 2023.

A cewarsa tsohon Gwamnan na Jihar Lagas nagartaccen dan siyasa ne wanda ke da kwarewa da gogewar shugabanci, sanin ciki da wajen matsalolin al’umma, lakantar hanyoyin magance su da sanin makamar iya hada kan kasa da fahimtar juna a tsakanin addinai.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Sanda A Harin Da Suka Kai Ofishin INEC A Enugu

 

ADVERTISEMENT

Bakin- Zuwo wanda kuma fitaccen dan kasuwar Kasa da Kasa ne ya bayyana hakan ne a tattaunawarsa da manema labarai a Sakkwato a rangadin tallata takarar Tinubu yana cewar a kungiyar TSO a karkashin jagorancin Shugabanta na Kasa (DG) Hon. Aminu Sulaiman su kan shiga lungu da sakon Kasar nan domin yada kyawawan manufofi da kudurorin Tinubu ga al’ummar Kasar nan sama da kowace kungiya.

Ya ce “Nijeriya na bukatar hazikin gwarzon shugaba mai gaskiya da adalci wanda zai bunkasa tattalin arziki, inganta haraji, habaka kasuwanci, fitowa da hanyoyin rage dogaro da man fetur, karawa Jihohi kason wata- wata na Gwamnatin Tarayya da uwa uba kammala hobbasar kwazon Shugaba Buhari wajen kawar da matsalolin tsaro da yaki da ta’addanci.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

Ya kara da cewar “Gagarumar karbuwar da Jagaban ya samu daga Arewaci da Kudancin Kasar nan babbar alama ce ta samun nasararsa ta zama Magajin Shugaba Buhari ta hanyar yi wa jam’iyyun adawa bugun ‘ya’yan kadanya wanda muna da tabbacin a budadden mulkinsa za a samu yadda da aminci a tsakanin Gwamnati da wadanda ake mulki.”

“Idan a na maganar karbuwa Tinubu a Nijeriya, Kano ba a ma maganarta domin 100 bisa 100 Kanawa za su zazzaga masa ruwan kuri’u kuma kowa ya san tasiri da girman kuri’un Kano a siyasar Nijeriya, hatta nan Sakkwato da take Jihar PDP, kuma Jihar shugaban yekuwar neman zaben PDP, za mu ba Atiku da Tambuwal mamaki in sha Allah.” In ji shi.

A cewar Bakin- Zuwo, Tinubu jagora ne nagari mai kima da tasiri, mai fada da cikawa wanda a kodayaushe ci- gaba da bunkasar al’umma shine burinsa don haka zabensa a matsayin Shugaban Kasa zabe ne na gina kasa, inganta jin dadi da walwalar jama’a, yaki da fatara, bunkasa noma da kiyo, inganta wutar lantarki, farfado da masana’antu, bunkasa hanyoyin kirkirar sababbin abubuwa ta hanyar inganta kimiya da fasaha da shigowar masu zuba jari tare da magance matsalolin ilimi da kiyon lafiya tare da shayar da al’umma romon mulkin Dimokuradiyya a dukkanin matakai.

tinubu
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    2027:Cece-kuce Ta Barke Tsakanin Tinubu Da Atiku
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Yadda Rikici Ya Tsananta Tsakanin Dan Daba Da Malaman Addini A Sakkwato
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Dalilin Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Yankin Sakkwato
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Atiku Ya Koka Kan Ƙaruwar Ta’addanci A Sakkwato

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
tinubu
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
DSS Ta Mamaye CBN, Ta Kwace Ragamar Ofishin Emefiele

DSS Ta Mamaye CBN, Ta Kwace Ragamar Ofishin Emefiele

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.