Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ƙaddamar da cibiyar Fasaha ta Zamani ta Arewa maso Yamma da hukumar sadarwa ta ƙasa (NCC) ta gina a Kano, wadda matasa suka lalata a lokacin zanga-zangar ƙuncin rayuwa ta #EndBadGovernance a watan Agustan 2024. Ministan Harkokin Sadarwa Dr. Bosun Tijani, ne ya wakilci shugaban ƙasa a wajen bikin ƙaddamarwar.
A jawabin sa, Minista Tijani ya bayyana cewa wannan katafaren aiki da gwamnatin Tinubu ta samar ƙarƙashin shirin Renewed Hope Agenda, zai iya zama babbar hanya ga matasa su tsira daga talauci idan har suka yi amfani da damar yadda ya kamata. Ya bayyana damuwarsa kan lalata cibiyar mako guda kafin a ƙaddamar da ita, duk da cewa an kammala aikin tun watan Janairu.
- Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
- 2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu
Ministan ya ce lokacin da ya samu labarin lalata cibiyar, bai bar fushinsa ya hana shi sake ci gaba da aikinta ba. Ya tuntuɓi kamfanoni kai tsaye don a gyara cibiyar cikin gaggawa ba tare da dogon tsarin gwamnati ba. Ya kara da cewa shirin cibiyar na da burin samar da ƙwararrun matasa miliyan uku da za su samu horo a fannin fasaha, domin samun damar ci gaba da kuma shiga kasuwannin duniya.
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ta bakin mataimakinsa Abdussalam Gwarzo, ya ce jihar na da shirin horas da matasa 300,000 kan fasahar zamani nan da shekarar 2027. Ya bayyana cewa tuni aka fara horar da ma’aikatan gwamnati 5,000 da suka samu ƙwarewa a fannin fasaha. Shugaban hukumar NCC, Dr. Aminu Maida, ya ce wannan cibiya ta fasaha na daga cikin dabarun raya tattalin arziƙin dijital na ƙasa, kuma za ta taimaka matuƙa wajen haɓaka ƙwarewar matasan jihar Kano.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp