ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

by Sani Anwar
1 year ago
2027

Wasu jiga-jigan ‘yan adawa a Nijeriya, karkashin kungiyar hadaka ta ‘Nigeria National Coalition Group’ (NNCG), na ci gba da kokarin tabbatar da wata hadaka mai karfin gaske da nufin kawar da gwamnatin APC, karkashin jagorncin Bola Ahmed Tinubu.

Wadannan ‘yan hamayya, sun samar da wata kungiyar hadaka da aka yi wa lakabi da ‘All Democratic Alliance (ADA)’, wadda suka aike wa hukumar zabe ta kasa da zummar yi mata rajista, domin zama jam’iyyar siyasa.

  • Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 
  • 2027: An Samu Ruɗani Kan Buƙatar Yi Wa ADA Rajista Don Ta Zama Jam’iyya

Kazalika, tun a farkon wannan shekara ne ‘yan mahayyar suka fara tunanin kafa wata hadaka, domin cimma wannan kudiri nasu da suka sanya a gaba.

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, wasikar wadda suka aika zuwa ga shugaban Hukumar Zabe ta Kasar (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, a ranar 19 ga watan Yuni, shugaban jam’iyyar hadakar ADA na kasa, Cif Akin Ricketts da Sakataren riko, Abdullahi Musa Elayo ne suka sanya mata hannu, sannan kuma Hukumar Zaben ta Kasa (INEC), ta karba a ranar 20 ga watan Yunin da muke ciki.

Har ila yau, kawancen hadakar na kunshe ne da jiga-jigan ‘yan hamayya a fagen siyasar wannan kasa da suka fito daga bangarorin kasar nan daban-daban, daga kuma mabambantan addinai.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Wannan ne ma dalilin da yasa wasu ke ganin hadakar za ta iya yin karfi kwarai da gaske, kasancewar ta samu wakilci a sassa daban-daban na wannan kasa.

Dalili kuwa shi ne, ‘yansiyasa ne da a baya suka samu damar rike manya-mnyan mukamai, sannan kuma har zuwa yanzu yana da tasiri a fagen siyasar kasar yadda ya kamata.

Manya-manyan jiga-jigan da ake gani a cikin wannan sabuwar tafiya ta hadakar jam’iyyar sun hada da:

Jagoran adawa a kasar, wanda a baya ya sha yin takarar shugabancin kasa, sannan kuma ko a shekarar 2023 shi ne ya zo na biyu bayan da ya samu kuri’a kusan miliyan bakwai.

Alhaji Atiku Abubakar, wanda a yanzu dan jam’iyyar PDP ne; ya kasance guda kuma jigo a siyasar Nijeriya, tun lokacin da ya zama mataimakin shugaban kasa, Cif Olusegun Obasanjo a shekarar 1999 zuwa 2007.

Tsohon mataimakin shugaban kasar, wanda ya fito daga Jihar Adamawa da ke Arewa maso gabashin Nijeriya, Bafulatani ne da ake yi wa kallon daya daga cikin masu matukar tasiri a fagen siyasar Nijeriya.

Atiku, na daga cikin fitattun mutanen da suka kulla wannan hadaka da ta haifar da jam’iyyar APC a shekarar 2014, da ta yi nasarar kwace mulki daga hannun jam’iyyar PDP a 2015.

A halin da ake ciki yanzu dai, jam’iyyar PDP na da gwamnoni kimanin 10 a fadin wannan kasa, koda-yake dai kuma, har yanzu babu gwamnan da ya bayyana amincewa da bin Atikun zuwa sabuwar jam’iyyar hadakar, duk da dai ana ganin watakila ficewar tasa za ta sa wasu daga cikin gwamnonin ficewa su su bi shi.

Haka zalika, tsohon dan takarar shugaban kasar na jam’iyyar LP, na daya daga cikin mutane na gaba-gaba a kafa wannan sabuwar tafiyar ta jam’iyyar ADA.

Peter Obi , wanda tsohon Gwamnan Jihar Anambra ne, ya kasance na uku a zaben shugaban kasar da ta gabata a 2023, inda ya samu kuri’a fiye da miliyan shida.

Obi, dan asalin kabilar Igbo ne daga Kudu maso gabashin wannan kasa, wanda da ya samu farin jini yadda ya kamata, musamman a tsakanin ‘yan kabilarsa.

Wannan dalili ne ma yasa ake ganin jam’iyyar tasa ta LP ta samu nasara a jihohin kasar nan 12, ciki har da Jihar Legas da Abuja a zaben shugaban kasar na 2023.

Kazalika, jam’iyyarsa ta LP na da gwamnan guda daya a Jihar Abia, sannan kuma ana ganin watakila ya bi shi cikin wannan sabuwar hadaka da ake shirin yi.

Har wa yau, a watan Maris da ya gabata ne Malam Nasiru el-Rufai ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC tare da kuma da komawa jam’iyyar SDP.

Tsohon gwamnan, ya kasance Ministan Abuja a tsakanin shekara ta 2003 zuwa 2007, kafin ya zama gwamnan Jihar Kaduna da ke Arewa maso yammacin kasar, na tsawon wa’adi biyu, wato tsakanin 2015 zuwa 2023.

Fitaccen ɗan siyasar, a kakar zaben 2023; wanda Bahaushe ne dan asalin garin Zaria, ya kasance na gaba-gaba wajen goyon bayan Bola Ahmed Tinubu na APC.

Sai dai kuma, bayan lashe zaben na Tinubu; sai kuma baraka ta kunno kai a tsakaninsa da Nasiru, bayan da majalisar dattawa ta ki amincewa da tantance shi, domin ba shi mukamin minista a gwamnatin ta Tinubu.

Rotimi Amaechi, shi ma guda ne cikin tsofaffin hannu a bangaren siyasar wannan kasa, domin kuwa ya kasance tsohon Gwamnan Jihar Ribas mai arzikin mai fetur da ke yankin Kudu maso kudancin wannan kasa daga 2007 zuwa 2015.

Haka nan, bayan kammala wa’adinsa a matsayin Gwamnan Jihar Ribas din, tsohon shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari ya nada shi ministan sufuri na tsawon shekara takwas daga 2015 zuwa 2023.

Har ila yau, A shekarar 2022 ya bayyana anisarya ta tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2023, to amma kuma sai ya sha kaye a hannun Tinubu a zaben fitar da gwani.

A wata hira da ya yi da BBC a baya-bayan nan, tsohon ministan ya ce; a shirye yake domin shiga duk wata hadakar da za ta kawar da gwamnatin Tinubu a halin yanzu.

A gefe guda kuma, Rauf Aregbesola ya taba rike mukamin Gwamnan Jihar Osun da ke Kudu maso yammacin Nijeriya, har na tsawon wa’adi biyu daga 2010 zuwa 2018.

A shekarar 2019, tsohon shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari ya nada shi, mukamin ministan harkokin cikin gida, mukamin da ya rike har 2023.

Aregbesola Bayerabe ne da ya fito daga yankin Kudu maso yammacin Nijeriya.

A farkon shekarar nan ne, Rauf Aregbesola ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar ta APC.

Tsohon jami’in soji, wanda ya taba zama Gwamnan Mulkin Soji na Jihar Neja daga 1984 zuwa 1986, Dabid Mark; dan asalin Jihar Benuwai ne.

Kazalika, ya rike mukamin ministan sadarwa; kafin ya zama dan majalisar dattawa mai wakiltar Benuwai ta Kudu a cikin jihar ta Benuwai.

Har ila yau, shi ne Shugaban Majalisar Dattawa mafi jimawa a mukamin, bayan jagorantar majalisar na tsawon wa’adi biyu, wato shekara takwas daga 2007 zuwa 2015.

Sannan, ya kasance dan asalin kabilar Idoma daga yankin Arewa ta tsakiyar Nijeriya, shi ma yana cikin wannan hadakar jam’iyyar adawa, dumu-dumu.

2027
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa
Siyasa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Next Post
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.