• English
  • Business News
Tuesday, June 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Binciki Kuɗaɗen Da Yake Bai Wa Gwamnoni – Sheikh Yakubu Musa

by El-Zaharadeen Umar
11 months ago
in Labarai
0
Tinubu Ya Binciki Kuɗaɗen Da Yake Bai Wa Gwamnoni – Sheikh Yakubu Musa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kungiyar Izala na Jihar Katsina, Sheikh Yakubu Musa Hassan, ya yi kira ga shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu, da ya binciki kuɗaɗen da abinci da ake bai wa gwamnonin jihohi domin raba wa talakawa.

Malamin ya bayyana haka ne, a lokacin da yake amsa tambayoyin manema labarai a gidansa da ke Katsina, dangane da zanga-zangar yunwa da matsin rayuwa da matasa ke yi a Nijeriya.

  • Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 
  • Ndume Ya Ba Ganduje Haƙuri Kan Kalaman Da Ya Yi Kan Tinubu Da Suka Yi Sanadin Sauke Shi

Malamin ya ƙara da cewa gaskiyar magana ita ce wannan taimako shugaba Tinubu yake bayarwa baya kai wa da talakawa.

Haka kuma ya yi kira ga waɗanda aka ɗora wa amanar al’umma musamman gwamnoni da su ji tsoron Allah wajen rabon tallafin da Gwamnatin Tarayya ke bayarwa.

“Ina kira ga ‘yan siyasa da kada su riƙa boye abincin da ake ba su, suna siyasa da shi, ina so ku sani, hatta ayyukan tituna da kuke yi idan yunwa ta kashe mutane wa za ku yi wa aikin?” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

A cewarsa, a irin wannan yanayi da ƙasa da al’umma suka tsinci kansu, ya kamata a ɗebo kuɗi daga ko ina domin magance wannan matsala ta yunwa da matsin rayuwa da jama’a ke fama da ita.

Kazalika, ya ce duk gwamnan da aka bai wa irin wannan kuɗaɗen da kayan abinci domin a fitar da al’umma daga cikin wannan yanayi, ya ce su ji tsoron Allah su isar da wannan sako ga waɗanda abin shafa.

Da juya kan batun zanga-zanga, malamin ya ce akwai takaici irin yadda matasa suka koma barayi suna kwashe duniyoyin al’umma da sunan zanga-zanga.

Ya yi kira ga jami’an tsaro da su tabbatar sun kama duk wanda ya taɓa kayan jama’a domin gurfanar da shi a gaban kuliya.

“Irin wannan abubuwan ne muka hango tun kafin a fara wannan zanga-zanga amma wasu suka riƙa zagin Malamai cewa an ba su kuɗi ne su hana matasa yin zanga-zanga, a zahirin gaskiya maganar ba haka ta ke ba,” a cewarsa.

Ya ƙara jaddada cewa lallai ya kamata Gwamnatin Tarayya da kuma na jihohi da sake karatun ta nutsu kan batun matas, a yi sabon tunani game da makomarsu ta hanyar fitowa da sabbin tsare-tsare na gwamnatin domin koya masu sana’a da ba su jari.

Ya ce a matsayinsu na malamai duk abin da ya taso suna iya baƙin ƙoƙarinsu domin ganin an warware komai cikin maslaha.

Malamin ya ce ‘yan jaridu suna da muhimmiyar rawar da za su taka wajen ganin an kawo karshen wannan zanga-zanga fiye da gwamnati da kuma jami’an tsaro.

Ya ƙara da cewa idan ‘yan jaridu suka yi amfani da alƙalumansu da hikimar da Allah Ya ba su, lallai za su iya kashe wutar zanga-zangar ake yi a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BincikeGwamnoniIzalaKatsinaMalamiMatasaTallafiTinubuZanga-zanga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kamala Harris Ta Zabi Tim Walz A Matsayin Mataimaki Kafin Shiga Zaben Amurka 

Next Post

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Ware Biliyan 19 Don Sanya Wa Lawal Kayan Girki

Related

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

6 hours ago
EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2
Labarai

EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

6 hours ago
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga
Labarai

Gargaɗin Amurka: Gwamnati Ta Bayar Da Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja

7 hours ago
Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago
Manyan Labarai

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

10 hours ago
Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

12 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe

15 hours ago
Next Post
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Ware Biliyan 19 Don Sanya Wa Lawal Kayan Girki

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Ware Biliyan 19 Don Sanya Wa Lawal Kayan Girki

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

June 23, 2025
EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

June 23, 2025
Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

June 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gargaɗin Amurka: Gwamnati Ta Bayar Da Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja

June 23, 2025
Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya

Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya

June 23, 2025
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

June 23, 2025
Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin

Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin

June 23, 2025
CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026

CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026

June 23, 2025
Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

June 23, 2025
Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

June 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.