• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Himmatu Wajen Rage Raɗaɗin Da ‘Yan Nijeriya Ke Ciki, In Ji Minista

by Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Tinubu Ya Himmatu Wajen Rage Raɗaɗin Da ‘Yan Nijeriya Ke Ciki, In Ji Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Shugaba Bola Tinubu ya ƙudiri aniyar rage raɗaɗin da ‘yan Nijeriya ke ciki.

 

Idris ya bayyana haka ne a ranar Lahadi a Kaduna a shirin ‘Hannu Da Yawa’ na Gidan Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN), Sashen Hausa.

  • An Bukaci Amurka Da Ta Inganta Hadin Gwiwa Da Kasar Sin Kan AI
  • Katsewar Wutar Lantarki: Mun Yi Asarar Fiye Da Naira Biliyan 6 – KEDCO 

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa ministan ya yi magana kan wahalar da aka samu sakamakon cire tallafin man fetur, kuma ya ce tallafin yana amfanar wasu tsirarun mutane ne kawai.

 

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

Lauyoyin Natasha Sun Buƙaci Ta Koma Majalisa Ranar Talata Bayan Miƙa Takardun Hukuncin Kotu

Ya ba da tabbacin cewa tattalin arzikin ƙasar nan zai daidaita, kuma babu wata gwamnati da za ta so a samu ci-baya a zamanin ta.

 

Idris ya jaddada cewa abin da ya kamata a gyara a ƙasar nan ba ya ta’allaƙa ne ga Majalisar Dokoki ta Ƙasa, wakilai da aka zaɓa ko kuma masu zartaswa na gwamnati kawai ba ne, amma har ga duk ‘yan Nijeriya ne.

 

Ya yi nuni da cewa a kwanakin baya Tinubu ya umurci ministoci da su rage kuɗin gudanar da mulki ta hanyar taƙaita yawan motocin su a lokacin da suke gudanar da ayyukan su da kuma yawan ma’aikatan su a lokacin tafiye-tafiye.

 

Idris ya ce, “Shugaba Tinubu yana nuna buƙatar a sauya daga yadda ake tafiyar da al’amura a Nijeriya.

 

“A duk lokacin da muka zauna taron Majalisar Zartaswa ta Tarayya (FEC), abin da Shugaban Ƙasa ke jaddadawa shi ne buƙatar a rage kashe kuɗaɗe da yawa waɗanda ba su zama dole ba wajen gudanar da mulki.

 

“Shugaba Tinubu har ma ya ba da sanarwa kan kuɗin tafiya da yawan ababen hawa. Ana iya ganin wannan a matsayin abu ƙanƙani, amma a zahiri yana da muhimmanci.”

 

Ministan ya ce ta fuskar noma, Tinubu ya ce an canja wa Ma’aikatar Noma da Raya Karkara suna zuwa Ma’aikatar Noma Da Samar Da Abinci ta yadda za a magance matsalolin noma ta ɓangarori daban-daban.

 

Haka zalika ya bayyana cewa Tinubu na magance matsalolin rashin tsaro kai-tsaye, inda ya ƙara da cewa tun kafin zuwan gwamnatin sa ne ake fuskantar matsalolin.

 

Idris ya ƙara da cewa har yanzu Gwamnatin Tarayya tana kan hanyar samar da dandamali da kuma tabbatar da jin daɗin jami’an tsaro domin inganta tsarin tsaron ƙasa.

 

Ya ƙara da cewa har yanzu Shugaban Ƙasa na neman shawarwari kan ba samar da ‘yan sandan jihohi.

 

Da yake ƙarin bayani, Idris ya ce ɗauke wutar lantarki da aka yi a sassan arewacin ƙasar nan kwanan nan ba wani shiri ne aka yi ba kamar yadda wasu suke cewa.

 

Ya nanata cewa babu wani shugaba da zai so da gangan al’ummar sa su kasance cikin halin rashin wutar lantarki da sauran matsaloli.

 

Ministan ya ƙara da cewa, “Shugaban Ƙasa yana bakin ƙoƙarin sa wajen ganin an samar da dauwamammiyar mafita kan matsalar lalacewar wuta a ƙasar nan.

 

“Haka nan ana gab da kammala aikin bututun iskar gas na AKK wanda zai taimaka wajen inganta masana’antu a Arewa.”

 

Idris ya buƙaci jama’a da su riƙa amfani da kafafen sadarwa na zamani wajen yaɗa labaran ƙasar nan ta hanyar da ta dace, yana kokawa da yadda ake yaɗa labaran ƙarya.

 

Ministan, yayin da ya yarda cewa lamari ne da ya shafi duniya, ya buƙaci yin amfani da kafafen ta hanya mai kyau.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kuncin rayuwaTabarbarewar Tattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

CIIE Ya Tabbatar Da Matsayin Kasar Sin A Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

Me Ya Faru Gwamna Abba Yusuf Ya Daina Ɗaukar Wayar Kwankwaso?

Related

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

55 minutes ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Lauyoyin Natasha Sun Buƙaci Ta Koma Majalisa Ranar Talata Bayan Miƙa Takardun Hukuncin Kotu

58 minutes ago
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

15 hours ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

16 hours ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

18 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

19 hours ago
Next Post
Me Ya Faru Gwamna Abba Yusuf Ya Daina Ɗaukar Wayar Kwankwaso?

Me Ya Faru Gwamna Abba Yusuf Ya Daina Ɗaukar Wayar Kwankwaso?

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

July 12, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Lauyoyin Natasha Sun Buƙaci Ta Koma Majalisa Ranar Talata Bayan Miƙa Takardun Hukuncin Kotu

July 12, 2025
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

July 12, 2025
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.