• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Himmatu Wajen Rage Raɗaɗin Da ‘Yan Nijeriya Ke Ciki, In Ji Minista

by Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
Tinubu Ya Himmatu Wajen Rage Raɗaɗin Da ‘Yan Nijeriya Ke Ciki, In Ji Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Shugaba Bola Tinubu ya ƙudiri aniyar rage raɗaɗin da ‘yan Nijeriya ke ciki.

 

Idris ya bayyana haka ne a ranar Lahadi a Kaduna a shirin ‘Hannu Da Yawa’ na Gidan Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN), Sashen Hausa.

  • An Bukaci Amurka Da Ta Inganta Hadin Gwiwa Da Kasar Sin Kan AI
  • Katsewar Wutar Lantarki: Mun Yi Asarar Fiye Da Naira Biliyan 6 – KEDCO 

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa ministan ya yi magana kan wahalar da aka samu sakamakon cire tallafin man fetur, kuma ya ce tallafin yana amfanar wasu tsirarun mutane ne kawai.

 

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Ya ba da tabbacin cewa tattalin arzikin ƙasar nan zai daidaita, kuma babu wata gwamnati da za ta so a samu ci-baya a zamanin ta.

 

Idris ya jaddada cewa abin da ya kamata a gyara a ƙasar nan ba ya ta’allaƙa ne ga Majalisar Dokoki ta Ƙasa, wakilai da aka zaɓa ko kuma masu zartaswa na gwamnati kawai ba ne, amma har ga duk ‘yan Nijeriya ne.

 

Ya yi nuni da cewa a kwanakin baya Tinubu ya umurci ministoci da su rage kuɗin gudanar da mulki ta hanyar taƙaita yawan motocin su a lokacin da suke gudanar da ayyukan su da kuma yawan ma’aikatan su a lokacin tafiye-tafiye.

 

Idris ya ce, “Shugaba Tinubu yana nuna buƙatar a sauya daga yadda ake tafiyar da al’amura a Nijeriya.

 

“A duk lokacin da muka zauna taron Majalisar Zartaswa ta Tarayya (FEC), abin da Shugaban Ƙasa ke jaddadawa shi ne buƙatar a rage kashe kuɗaɗe da yawa waɗanda ba su zama dole ba wajen gudanar da mulki.

 

“Shugaba Tinubu har ma ya ba da sanarwa kan kuɗin tafiya da yawan ababen hawa. Ana iya ganin wannan a matsayin abu ƙanƙani, amma a zahiri yana da muhimmanci.”

 

Ministan ya ce ta fuskar noma, Tinubu ya ce an canja wa Ma’aikatar Noma da Raya Karkara suna zuwa Ma’aikatar Noma Da Samar Da Abinci ta yadda za a magance matsalolin noma ta ɓangarori daban-daban.

 

Haka zalika ya bayyana cewa Tinubu na magance matsalolin rashin tsaro kai-tsaye, inda ya ƙara da cewa tun kafin zuwan gwamnatin sa ne ake fuskantar matsalolin.

 

Idris ya ƙara da cewa har yanzu Gwamnatin Tarayya tana kan hanyar samar da dandamali da kuma tabbatar da jin daɗin jami’an tsaro domin inganta tsarin tsaron ƙasa.

 

Ya ƙara da cewa har yanzu Shugaban Ƙasa na neman shawarwari kan ba samar da ‘yan sandan jihohi.

 

Da yake ƙarin bayani, Idris ya ce ɗauke wutar lantarki da aka yi a sassan arewacin ƙasar nan kwanan nan ba wani shiri ne aka yi ba kamar yadda wasu suke cewa.

 

Ya nanata cewa babu wani shugaba da zai so da gangan al’ummar sa su kasance cikin halin rashin wutar lantarki da sauran matsaloli.

 

Ministan ya ƙara da cewa, “Shugaban Ƙasa yana bakin ƙoƙarin sa wajen ganin an samar da dauwamammiyar mafita kan matsalar lalacewar wuta a ƙasar nan.

 

“Haka nan ana gab da kammala aikin bututun iskar gas na AKK wanda zai taimaka wajen inganta masana’antu a Arewa.”

 

Idris ya buƙaci jama’a da su riƙa amfani da kafafen sadarwa na zamani wajen yaɗa labaran ƙasar nan ta hanyar da ta dace, yana kokawa da yadda ake yaɗa labaran ƙarya.

 

Ministan, yayin da ya yarda cewa lamari ne da ya shafi duniya, ya buƙaci yin amfani da kafafen ta hanya mai kyau.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kuncin rayuwaTabarbarewar Tattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

CIIE Ya Tabbatar Da Matsayin Kasar Sin A Tattalin Arzikin Duniya

Next Post

Me Ya Faru Gwamna Abba Yusuf Ya Daina Ɗaukar Wayar Kwankwaso?

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

27 minutes ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

1 hour ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

2 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

4 hours ago
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja
Labarai

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

5 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

6 hours ago
Next Post
Me Ya Faru Gwamna Abba Yusuf Ya Daina Ɗaukar Wayar Kwankwaso?

Me Ya Faru Gwamna Abba Yusuf Ya Daina Ɗaukar Wayar Kwankwaso?

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.