• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Isa Japan Don Halartar Taron TICAD9

by Abubakar Sulaiman
2 months ago
in Manyan Labarai
0
Tinubu Ya Isa Japan Don Halartar Taron TICAD9
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya isa ƙasar Japan a wani muhimmin ziyarar aikin ƙasa da ƙasa domin halartar taron Tokyo International Conference on African Development (TICAD9) karo na tara.

Shugaba Tinubu ya sauka a filin jirgin sama na Haneda, Tokyo, da misalin ƙarfe 12:55 na safe agogon ƙasar Japan a ranar Talata, inda Jakadan TICAD, Hideo Matsubara, ya tarɓe shi. Wannan shi ne karo na farko da Shugaban Nijeriyar zai kai ziyara ta aiki a Japan tun bayan hawansa karagar mulki watanni 25 da suka gabata.

  • Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda
  • Fim Na Kisan Kiyashin Da Sojojin Japan Suka Yi A Birnin Nanjing Na Samun Karbuwa A Kasar Sin

A birnin Yokohama, Tinubu zai yi amfani da taron wajen gabatar da Nijeriya a matsayin cibiyar zuba jari ga ƴan kasuwar Japan, musamman waɗanda suke da harkoki a Nijeriya da kuma masu sha’awar shiga kasuwanci a fannoni daban-daban. Haka kuma zai halarci zaman taruka, ya gana da shugabannin ƙasashe da manyan ƴan kasuwa daga Japan.

Taron na bana, mai taken “Co-create Innovative Solutions with Africa,” na nufin ƙarfafa haɗin kai tsakanin Afirka da Japan, tare da samar da mafita ta hanyar sabbin fasahohi da ingantattun shirye-shirye. TICAD na taka muhimmiyar rawa wajen ƙarfafa ci gaba mai ɗorewa, da haɓaka jarin fannoni masu zaman kansu da kuma gina muhimman cibiyoyi a nahiyar Afrika.

Tun daga kafuwarsa a 1993, TICAD ke zama babban dandalin tattaunawa tsakanin Japan da Afrika, wanda ake gudanarwa duk bayan shekaru uku, a Japan ko a wata ƙasa ta Afrika. Taron da ya gabata an gudanar da shi ne a Tunisia a 2022, yayin da wannan karo na 2025 ke gudana daga 20 zuwa 22 ga watan Agusta, inda shugabannin Afrika, da abokan cigaba, da ƴan kasuwa da ƙungiyoyin fararen hula ke halarta domin samar da hanyoyin bunƙasa tattalin arziƙi da ɗorewar zaman lafiya a nahiyar.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JapanTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke

Next Post

An Kaddamar Da Ayyukan Tsara Shirin Bidiyo Na “Yawo A Sin: Hainan Mai Kuzari”

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

6 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

8 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

1 day ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

1 day ago
Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa
Manyan Labarai

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

2 days ago
Next Post
An Kaddamar Da Ayyukan Tsara Shirin Bidiyo Na “Yawo A Sin: Hainan Mai Kuzari”

An Kaddamar Da Ayyukan Tsara Shirin Bidiyo Na “Yawo A Sin: Hainan Mai Kuzari”

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.