• English
  • Business News
Thursday, September 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Isa Japan Don Halartar Taron TICAD9

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago
in Manyan Labarai
0
Tinubu Ya Isa Japan Don Halartar Taron TICAD9
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya isa ƙasar Japan a wani muhimmin ziyarar aikin ƙasa da ƙasa domin halartar taron Tokyo International Conference on African Development (TICAD9) karo na tara.

Shugaba Tinubu ya sauka a filin jirgin sama na Haneda, Tokyo, da misalin ƙarfe 12:55 na safe agogon ƙasar Japan a ranar Talata, inda Jakadan TICAD, Hideo Matsubara, ya tarɓe shi. Wannan shi ne karo na farko da Shugaban Nijeriyar zai kai ziyara ta aiki a Japan tun bayan hawansa karagar mulki watanni 25 da suka gabata.

  • Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda
  • Fim Na Kisan Kiyashin Da Sojojin Japan Suka Yi A Birnin Nanjing Na Samun Karbuwa A Kasar Sin

A birnin Yokohama, Tinubu zai yi amfani da taron wajen gabatar da Nijeriya a matsayin cibiyar zuba jari ga ƴan kasuwar Japan, musamman waɗanda suke da harkoki a Nijeriya da kuma masu sha’awar shiga kasuwanci a fannoni daban-daban. Haka kuma zai halarci zaman taruka, ya gana da shugabannin ƙasashe da manyan ƴan kasuwa daga Japan.

Taron na bana, mai taken “Co-create Innovative Solutions with Africa,” na nufin ƙarfafa haɗin kai tsakanin Afirka da Japan, tare da samar da mafita ta hanyar sabbin fasahohi da ingantattun shirye-shirye. TICAD na taka muhimmiyar rawa wajen ƙarfafa ci gaba mai ɗorewa, da haɓaka jarin fannoni masu zaman kansu da kuma gina muhimman cibiyoyi a nahiyar Afrika.

Tun daga kafuwarsa a 1993, TICAD ke zama babban dandalin tattaunawa tsakanin Japan da Afrika, wanda ake gudanarwa duk bayan shekaru uku, a Japan ko a wata ƙasa ta Afrika. Taron da ya gabata an gudanar da shi ne a Tunisia a 2022, yayin da wannan karo na 2025 ke gudana daga 20 zuwa 22 ga watan Agusta, inda shugabannin Afrika, da abokan cigaba, da ƴan kasuwa da ƙungiyoyin fararen hula ke halarta domin samar da hanyoyin bunƙasa tattalin arziƙi da ɗorewar zaman lafiya a nahiyar.

Labarai Masu Nasaba

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JapanTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

PDP Ta Yi Fatali Da Sakamakon Zaɓen Cike Gurbi Na Okura, Ta Nemi A Soke

Next Post

An Kaddamar Da Ayyukan Tsara Shirin Bidiyo Na “Yawo A Sin: Hainan Mai Kuzari”

Related

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci
Manyan Labarai

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

3 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

8 hours ago
Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
Manyan Labarai

Mele Kyari Ya Bayyana A Ofishin EFCC Kan Zargin Badaƙalar Dala Biliyan 7.2

9 hours ago
Akwai Bukatar Tinubu Ya Rubanya Kokarin Buhari Na Bunkasa Harkokin Noma  -Alhaji Umar
Manyan Labarai

Ranar ‘Yancin Kai: Tinubu Zai Yi Wa ‘Yan Nijeriya Jawabi 1 Ga Oktoba

19 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Sojoji 5 Wasu Mutum 10 A Zamfara

21 hours ago
INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC
Manyan Labarai

INEC Ta Amince Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

22 hours ago
Next Post
An Kaddamar Da Ayyukan Tsara Shirin Bidiyo Na “Yawo A Sin: Hainan Mai Kuzari”

An Kaddamar Da Ayyukan Tsara Shirin Bidiyo Na “Yawo A Sin: Hainan Mai Kuzari”

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

Cutar Diphtheria Ta Kashe Yara 10 A Jihar Neja

September 11, 2025
DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

September 11, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

‘Yansanda Sun Cafke ‘Yan Fashi 3 A Kano, Sun Ƙwato Motar Sata

September 11, 2025
Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

Ganawata Da Macron Ta Yi Amfani – Tinubu

September 11, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

September 11, 2025
Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL

Mele Kyari Ya Bayyana A Ofishin EFCC Kan Zargin Badaƙalar Dala Biliyan 7.2

September 11, 2025
Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Amfani Da Karfin Tuwo Ba Zai Iya Kawo Zaman Lafiya A Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

Kasar Sin Ta Fitar Da Mizanin Cinikayya Tare Da Sauran Mambobin BRICS

September 10, 2025
Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

Mataimakin Shugaban Unilever: Mun Kudiri Aniyar Zama “Masu Tseren Gudun Fanfalaki” A Kasar Sin

September 10, 2025
Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

Shettima Ya Yaba Wa Uba Sani Kan Kafa Majalisar Ƙwarewa Ta Jihar Kaduna

September 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.