• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Karya Doka Kan Nada Olukoyede A Shugabancin Hukumar EFCC –Kwararru

by Abubakar Abba
2 years ago
Tinubu

Nada Mista Ola Olukoyede a matsayin shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi, hakan ya janyo cece-cekuce a ra’ayin wasu kwararru a Nijeriya.

A jiya ne dai, Tinubu ya nada Ola a matsayin sabon shugaban EFCC wanda zai shafe shekaru hudu kan kujerar EFCC, gabanin majalisar dattawa ta tabbatar da nadin nasa.

  • Tinubu Ya Nada Olukoyede A Matsayin Sabon Shugaban EFCC
  • Abubuwa 5 Game Da Sabon Shugaban EFCC, Ola Olukoyede

A cikin sanarwar da mai magana da yawun shugaban kasa Ajuri Ngelale ya fitar, ta ce, Tinubu ya nada Olukoyede ne bayan da tsohon shugaban EFCC, Abdulrasheed Bawa, ya yi ritaya a matsayin shugaban Hukumar.

Sai dai, wasu na tambaya kan halarcin nadin na Ola, musamman bisa la’akari da sashe na 2 (3) a cikin baka na dokar EFCC ta shekarar 2004 wadda ta nuna cewa, dole ne shugaban da za a nada a EFCC, ya kasance wanda yake kan bakin aiki ko kuma wanda ya yi ritaya a fannin tsaro na gwamnati ko ya kasance wanda ya taba yin aiki a wata hukumar tsaro, ya zama wanda yake da kwarewar aiki har ta tsawon shekaru 15.

Amma sai sanarwa Ngelale ta bayyana cewa, Tinubu ya nada Ola ne bisa karfin ikon da kudin tsarin mulkin Nijerya ya ba shi da kuma da yadda sashe na 2 (3) na dokar EFCC ta shekarar 2004 ta tanada.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Ngelale ya kara da cewa Ola, ya shafe sama da shekaru 22 yana aiki a matsayin kwararren lauya, inda ya ce, yana da kwarewa wajen tafiyar da ayyukan EFCC duba da ya taba rike mukamin shugaban ma’aikata a lokacin shugabancin tsohon shugaban EFCC Ibrahim Magu daga 2016 zuwa 2018 ya kuma taba rike mukamin sakataren Hukumar ta EFCC daga 2018 zuwa-2023 wanda hakan ya nuna cewa ya cancanci ya shugabanci EFCC.

Sai dai, an ruwaito Darakta a kungiyar Action Aid a Nijeriya, Andrew Mamedu, ya ce, Tinubu ya karya dokar da ta kafa Hukumar EFCC.

Shi kuwa wani kwararren lauya mai lambar kwarewa ta SAN, Victor Opara, ya ce, nadin ya yi daidai idan aka yi la’akari da sashi na 2 na dokar da ta kafa Hukumar ta EFCC.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Triumph
Manyan Labarai

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza
Labarai

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga
Labarai

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Next Post
Nijeriya Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur A 2024 —Kyari

Nijeriya Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur A 2024 —Kyari

LABARAI MASU NASABA

Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.