• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Karya Doka Kan Nada Olukoyede A Shugabancin Hukumar EFCC –Kwararru

by Abubakar Abba
2 years ago
in Labarai
0
Tinubu Ya Amince Da Biyan Ma’aikata Karin Albashin N35,000 Na Wucin Gadi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nada Mista Ola Olukoyede a matsayin shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi, hakan ya janyo cece-cekuce a ra’ayin wasu kwararru a Nijeriya.

A jiya ne dai, Tinubu ya nada Ola a matsayin sabon shugaban EFCC wanda zai shafe shekaru hudu kan kujerar EFCC, gabanin majalisar dattawa ta tabbatar da nadin nasa.

  • Tinubu Ya Nada Olukoyede A Matsayin Sabon Shugaban EFCC
  • Abubuwa 5 Game Da Sabon Shugaban EFCC, Ola Olukoyede

A cikin sanarwar da mai magana da yawun shugaban kasa Ajuri Ngelale ya fitar, ta ce, Tinubu ya nada Olukoyede ne bayan da tsohon shugaban EFCC, Abdulrasheed Bawa, ya yi ritaya a matsayin shugaban Hukumar.

Sai dai, wasu na tambaya kan halarcin nadin na Ola, musamman bisa la’akari da sashe na 2 (3) a cikin baka na dokar EFCC ta shekarar 2004 wadda ta nuna cewa, dole ne shugaban da za a nada a EFCC, ya kasance wanda yake kan bakin aiki ko kuma wanda ya yi ritaya a fannin tsaro na gwamnati ko ya kasance wanda ya taba yin aiki a wata hukumar tsaro, ya zama wanda yake da kwarewar aiki har ta tsawon shekaru 15.

Amma sai sanarwa Ngelale ta bayyana cewa, Tinubu ya nada Ola ne bisa karfin ikon da kudin tsarin mulkin Nijerya ya ba shi da kuma da yadda sashe na 2 (3) na dokar EFCC ta shekarar 2004 ta tanada.

Labarai Masu Nasaba

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Ngelale ya kara da cewa Ola, ya shafe sama da shekaru 22 yana aiki a matsayin kwararren lauya, inda ya ce, yana da kwarewa wajen tafiyar da ayyukan EFCC duba da ya taba rike mukamin shugaban ma’aikata a lokacin shugabancin tsohon shugaban EFCC Ibrahim Magu daga 2016 zuwa 2018 ya kuma taba rike mukamin sakataren Hukumar ta EFCC daga 2018 zuwa-2023 wanda hakan ya nuna cewa ya cancanci ya shugabanci EFCC.

Sai dai, an ruwaito Darakta a kungiyar Action Aid a Nijeriya, Andrew Mamedu, ya ce, Tinubu ya karya dokar da ta kafa Hukumar EFCC.

Shi kuwa wani kwararren lauya mai lambar kwarewa ta SAN, Victor Opara, ya ce, nadin ya yi daidai idan aka yi la’akari da sashi na 2 na dokar da ta kafa Hukumar ta EFCC.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EFCCOlukoyedeTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gidauniyar Ahmadu Bello Ta Gano Matsalolin Da Suka Addabi Ilimi A Arewa

Next Post

Nijeriya Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur A 2024 —Kyari

Related

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya
Labarai

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

10 hours ago
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025
Labaran Kasuwanci

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

13 hours ago
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista
Labarai

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

15 hours ago
Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi
Labarai

Gwamnan Katsina Ya Dakatar Da Ma’aikatan Gidan Gyaran Hali Saboda Azabtar Da Wani Matashi

17 hours ago
2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

18 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

19 hours ago
Next Post
Nijeriya Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur A 2024 —Kyari

Nijeriya Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur A 2024 —Kyari

LABARAI MASU NASABA

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

July 13, 2025
Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

July 13, 2025
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.