ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Karya Doka Kan Nada Olukoyede A Shugabancin Hukumar EFCC –Kwararru

by Abubakar Abba
3 years ago
Tinubu

Nada Mista Ola Olukoyede a matsayin shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi, hakan ya janyo cece-cekuce a ra’ayin wasu kwararru a Nijeriya.

A jiya ne dai, Tinubu ya nada Ola a matsayin sabon shugaban EFCC wanda zai shafe shekaru hudu kan kujerar EFCC, gabanin majalisar dattawa ta tabbatar da nadin nasa.

  • Tinubu Ya Nada Olukoyede A Matsayin Sabon Shugaban EFCC
  • Abubuwa 5 Game Da Sabon Shugaban EFCC, Ola Olukoyede

A cikin sanarwar da mai magana da yawun shugaban kasa Ajuri Ngelale ya fitar, ta ce, Tinubu ya nada Olukoyede ne bayan da tsohon shugaban EFCC, Abdulrasheed Bawa, ya yi ritaya a matsayin shugaban Hukumar.

ADVERTISEMENT

Sai dai, wasu na tambaya kan halarcin nadin na Ola, musamman bisa la’akari da sashe na 2 (3) a cikin baka na dokar EFCC ta shekarar 2004 wadda ta nuna cewa, dole ne shugaban da za a nada a EFCC, ya kasance wanda yake kan bakin aiki ko kuma wanda ya yi ritaya a fannin tsaro na gwamnati ko ya kasance wanda ya taba yin aiki a wata hukumar tsaro, ya zama wanda yake da kwarewar aiki har ta tsawon shekaru 15.

Amma sai sanarwa Ngelale ta bayyana cewa, Tinubu ya nada Ola ne bisa karfin ikon da kudin tsarin mulkin Nijerya ya ba shi da kuma da yadda sashe na 2 (3) na dokar EFCC ta shekarar 2004 ta tanada.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ngelale ya kara da cewa Ola, ya shafe sama da shekaru 22 yana aiki a matsayin kwararren lauya, inda ya ce, yana da kwarewa wajen tafiyar da ayyukan EFCC duba da ya taba rike mukamin shugaban ma’aikata a lokacin shugabancin tsohon shugaban EFCC Ibrahim Magu daga 2016 zuwa 2018 ya kuma taba rike mukamin sakataren Hukumar ta EFCC daga 2018 zuwa-2023 wanda hakan ya nuna cewa ya cancanci ya shugabanci EFCC.

Sai dai, an ruwaito Darakta a kungiyar Action Aid a Nijeriya, Andrew Mamedu, ya ce, Tinubu ya karya dokar da ta kafa Hukumar EFCC.

Shi kuwa wani kwararren lauya mai lambar kwarewa ta SAN, Victor Opara, ya ce, nadin ya yi daidai idan aka yi la’akari da sashi na 2 na dokar da ta kafa Hukumar ta EFCC.

Tinubu
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Nijeriya Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur A 2024 —Kyari

Nijeriya Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur A 2024 —Kyari

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.