ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Karya Doka Kan Nada Olukoyede A Shugabancin Hukumar EFCC –Kwararru

by Abubakar Abba
3 years ago
Tinubu

Nada Mista Ola Olukoyede a matsayin shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi, hakan ya janyo cece-cekuce a ra’ayin wasu kwararru a Nijeriya.

A jiya ne dai, Tinubu ya nada Ola a matsayin sabon shugaban EFCC wanda zai shafe shekaru hudu kan kujerar EFCC, gabanin majalisar dattawa ta tabbatar da nadin nasa.

  • Tinubu Ya Nada Olukoyede A Matsayin Sabon Shugaban EFCC
  • Abubuwa 5 Game Da Sabon Shugaban EFCC, Ola Olukoyede

A cikin sanarwar da mai magana da yawun shugaban kasa Ajuri Ngelale ya fitar, ta ce, Tinubu ya nada Olukoyede ne bayan da tsohon shugaban EFCC, Abdulrasheed Bawa, ya yi ritaya a matsayin shugaban Hukumar.

ADVERTISEMENT

Sai dai, wasu na tambaya kan halarcin nadin na Ola, musamman bisa la’akari da sashe na 2 (3) a cikin baka na dokar EFCC ta shekarar 2004 wadda ta nuna cewa, dole ne shugaban da za a nada a EFCC, ya kasance wanda yake kan bakin aiki ko kuma wanda ya yi ritaya a fannin tsaro na gwamnati ko ya kasance wanda ya taba yin aiki a wata hukumar tsaro, ya zama wanda yake da kwarewar aiki har ta tsawon shekaru 15.

Amma sai sanarwa Ngelale ta bayyana cewa, Tinubu ya nada Ola ne bisa karfin ikon da kudin tsarin mulkin Nijerya ya ba shi da kuma da yadda sashe na 2 (3) na dokar EFCC ta shekarar 2004 ta tanada.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Ngelale ya kara da cewa Ola, ya shafe sama da shekaru 22 yana aiki a matsayin kwararren lauya, inda ya ce, yana da kwarewa wajen tafiyar da ayyukan EFCC duba da ya taba rike mukamin shugaban ma’aikata a lokacin shugabancin tsohon shugaban EFCC Ibrahim Magu daga 2016 zuwa 2018 ya kuma taba rike mukamin sakataren Hukumar ta EFCC daga 2018 zuwa-2023 wanda hakan ya nuna cewa ya cancanci ya shugabanci EFCC.

Sai dai, an ruwaito Darakta a kungiyar Action Aid a Nijeriya, Andrew Mamedu, ya ce, Tinubu ya karya dokar da ta kafa Hukumar EFCC.

Shi kuwa wani kwararren lauya mai lambar kwarewa ta SAN, Victor Opara, ya ce, nadin ya yi daidai idan aka yi la’akari da sashi na 2 na dokar da ta kafa Hukumar ta EFCC.

Tinubu
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Nijeriya Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur A 2024 —Kyari

Nijeriya Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur A 2024 —Kyari

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.