Sashen samar da wadataccen abinci da ke karkashin kulawar Fadar Shugaban Kasa (PFSCU), a kwanan baya ne ya hada wani taron tattaunawa da manyan kafafen yada labarai da kuma ‘yan jarida, masu dauko rahotannin aikin noma na kasar nan.
An gudanar da tattaunawar ce a birnin tarayyar Abuja, da nufin hada karfi da karfe; domin kafafen yada labaran da kuma ‘yan jaridar da ke dauko labaran aikin noma, su bayar da goyon bayansu wajen yada rahotannin aikin samar da wadataccen abinci a kasar.
- Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
- Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don YaÆ™ar ‘Yan Ta’adda
A taron, an tattauna kan gudunmawar da kafafaen yada labaran za su bayar, musamman wajen wayar da kan ‘yan Nijeriya kan burin samar da wadatacen abinci a fadin kasar nan.
Marion Moon, mai taimakawa shuagaban kasa a bangaren aikin noma da kuma sashen na PFSCU, ya jadda muhimmancin kara mayar da hankali da gwamnatin mai ci ke kan yi, na kara habaka fannin aikin noma a kasar, musamman ta hanyar samar da trsare-tsare da kuma dabaru.
Ya sanar da cewa, ya zama wajibi Nijeriya ta cimma burin da ta sanya a gaba na samar da wadataccen abinci a kasar, inda ya kara cewa; hakan ne yasa aka jawo kafafen yada labaran, domin cimma wannan buri.
Wakilan kafafen yada labaran, sun tattauna kan kalubalen da fannin aikin noman kasar ke fuskanta da suka hada da rashin samar ainahin bayanai kan abin da ya shafi aikin noma.
Rashin bayar da ingantaccen dauki ga fannin daga bangaren gwamnati, kalubalen rashin tsaro da zabar wasu ‘yan lelen kafafen yada labarai, musaman da gwamnatin kasar ke yi, wajen bayar da tallace-tallacen da suka shafi bangaren aikin noma, inda suka yi nuni da cewa, kafafen yada labarai; sun dogara ne kacokan a kan samun tallace-tallace, wanda akasari shi ne ke rike da su.
Sun kuma bukaci a samar wa da kafafen yada labaran kasar, wata hanyar sadarwa ta bai daya, musamman domin su kara wallafa rahotannin da suka shafi ayyukan gwamnatin kasar na aikin noma.
Mahalarta taron, sun kuma amince da kara daga matsayin aikin noma na kasar, ciki har da bai wa ‘yan jarida horo a kai-kai kan abin da ya shafi wallafa rahotannin aikin noma.
Sahen na PFSCU, ya mayar da hankali ne wajen ganin yin hadaka da cibiyoyi, musamman domin gwamnatin tarayya ta cimma burin samar da wadataccen abinci a kasar da kuma kara habaka fannin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp