• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Kori Mele Kyari, Ya Naɗa Ojulari A Matsayin Shugaban NNPC

by Sadiq
1 month ago
in Manyan Labarai
0
Tinubu Ya Kori Mele Kyari, Ya Naɗa Ojulari A Matsayin Shugaban NNPC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba Bola Tinubu, ya sauke Mele Kyari daga muƙaminsa na Shugaban Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPC), tare da rushe kwamitin gudanarwarsa, daga ranar 2 ga watan Afrilu, 2025. 

Bayo Onanuga, mai magana da yawun shugaban ƙasa ne ya sanar da hakan, inda ya ce an ɗauki matakin ne domin inganta aiki da bunƙasa NNPC a matsayin kamfani mai zaman kansa.

  • Duk Da Hanin Gwamna Da ‘Yansanda, Natasha Ta Isa Gida Kuma Ta Yi Taro
  • Gwamnatin Edo Za Ta Biya Diyyar Mafarauta ‘Yan Kano 16 Da Aka Kashe A Uromi 

An naɗa Bayo Ojulari a matsayin sabon Shugaban Kamfanin, wanda zai maye gurbin Kyari, yayin da Ahmadu Musa Kida ya zama sabon Shugaban Kwamitin Gudanarwa.

Haka kuma, an naɗa Adedapo Segun a matsayin Babban Jami’in Kuɗi.

An kuma naɗa wasu shuwagabanni guda shida da ke wakiltar yankunan Nijeriya daban-daban, tare da wakilai biyu daga ma’aikatun Kuɗi da Albarkatun Man Fetur.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

Gwamnatin Tinubu na da burin jan hankalin masu zuba jari da kuɗi har dala biliyan 30 nan da 2027 da kuma dala biliyan 60 nan da 2030.

Hakazalika, tana shirin ƙara yawan haƙar ɗanyen mai zuwa ganga miliyan uku a kowace rana nan da 2030, tare da ƙara yawan samar da gas zuwa biliyan goma a kowace rana.

Shugaban ƙasa ya buƙaci sabbkn shugabancin NNPC da su ƙara ƙarfin tace mai a gida don rage dogaro da shigo da man fetur daga ƙasashen waje da kuma ƙarfafa tsaron makamashi a Nijeriya.

Kida, sabon Shugaban Kwamitin Gudanarwa, da Ojulari, sabon Shugaban Kamfanin, dukkaninsu ƙwararru ne a harkar man fetur.

Tinubu ya gode wa shugabannin da aka sauke bisa gudunmawar da suka bayar, musamman wajen farfaɗo da matatun mai na Fatakwal da Warri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Mele KyariNNPCTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Allah Ya Yi Wa Galadiman Kano, Abbas Sanusi, Rasuwa 

Next Post

Trump Na Son Yin Wa’adi Na Uku Na Shugabancin Amurka

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

6 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

12 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

17 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

21 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

22 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

2 days ago
Next Post
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Na Son Yin Wa'adi Na Uku Na Shugabancin Amurka

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.