Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya shiga tsakanin gwamnatin kano da ‘yan kasuwa a jihar kan rusau da gwamnati ke yi bayan ganawarsa da tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje.
Idan dai za a iya tunawa, Gwamna Abba Kabir Yusuf a cikin daren ranar Asabar ya rusa wasu gine-gine a Otal din Daula da kuma sansanin Hajji da ke cikin birnin Kano.
An rusa gine-gine na miliyoyin nairori kamar dai yadda aka rusa wani ginin kasuwa mai hawa uku da ke da shaguna 90 a kan titin Race Course, a unguwar GRA ta Nasarawa. Gwamnatin ta bayyana gine-ginen ne a matsayin haramtattu.
A ranar Asabar, Gwamna Yusuf ya jaddada aniyarsa ta ci gaba da rusa gine-ginen da gwamnatin ta yi imanin cewa haramtattu ne a jihar.
Wata sanarwa da babban sakataren yada labaran gwamnatin jihar Kano, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ta ce za a ci gaba da aikin rusau.
Bayan faruwar wannan lamarin, Gwamna Ganduje ya garzaya don ganawa da shugaban kasa a ranar Litinin a fadar shugaban kasa domin yi masa bayani kan irin abubuwan da ke faruwa a jihar ta Kano.
“Tinubu ya ba da umarnin a dakatar da rusau, hakan bai dace ba, yana haifar da asara ga ‘yan Nijeriya,” in ji wata majiyar da ta so a sakaya sunanta kuma tace Tinubu ne ya bayyana hakan.
Shugaba Tinubu, Ya kuma bukaci jami’an tsaro da su dakile duk wani yunkuri na cigaba da rusau din a Jihar.
Da aka tuntubi gaskiyar wannan batu da aka ce ya fito daga fadar shugaban kasa, Tofa ya shaida wa jaridar Politicsdigest cewa: “har yanzu ana ci gaba da rusau, gwamnati ta kuduri aniyar kwato kadarorin jama’a da aka sayar ko aka wawure.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp