• English
  • Business News
Monday, September 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

by Sulaiman
3 weeks ago
in Manyan Labarai
0
Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Tarayya ta ƙaryata zargin wai ana nuna bambanci wajen rabon ayyuka da naɗin muƙamai a ƙarƙashin shugabancin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, tana mai cewa babu wani yanki da aka ware, kowane ɓangare yana samun kulawa iri ɗaya.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya faɗa a cikin wata sanarwa a ranar Lahadi, cewa gwamnatin Tinubu tana tafiya ne bisa gaskiya, adalci da daidaito wajen rarraba ayyuka da damarmaki.

  • Kasar Sin Ta Inganta Wuraren Tunawa Da Tarihi Don Bikin Samun Nasara Kan Zaluncin Japanawa
  • Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike

Ya ce manyan ayyukan raya ƙasa suna gudana a dukkan yankuna shida, ciki har da tituna, gadaje, layin dogo, wutar lantarki da kuma cibiyoyin kula da lafiya fiye da 1,000 da aka gyara a faɗin ƙasar.

 

Labarai Masu Nasaba

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa

APC Da PDP Na Zargin Juna Kan Amfani Da Addini Wajen Neman Nasara A 2027

A cewar sa, yankin Arewa-maso-yamma ya samu kaso mafi girma na ayyuka da ya kai naira tiriliyan 5.97, Kudu-maso-kudu ya samu naira tiriliyan 2.41, Arewa-ta-tsakiya naira tiriliyan 1.13, Kudu-maso-gabas naira biliyan 407, Arewa-maso-gabas naira biliyan 400, yayin da Kudu-maso-yamma (ban da Legas) ya samu naira biliyan 604.

 

Idris ya ce dukkan waɗannan yankuna suna amfana da manyan hanyoyi, layukan dogo da kuma hukumomin raya yankuna.

 

Ministan ya ce daga cikin muhimman ayyukan da ake aiwatarwa akwai Titin Bakin Teku na Legas zuwa Kalaba, da Babban Titin Sakkwato zuwa Badagiri, da gyaran layin dogo daga Fatakwal zuwa Maiduguri, da kuma Hanyar Gadar Neja ta 2.

 

Haka kuma, gwamnati ta samar da fiye da naira biliyan 250 don ayyukan jirgin ƙasa a Kano da Kaduna, yayin da ake gudanar da ayyukan layin dogo na Cikin gari a Legas da Ogun. Gaba ɗaya, an ƙiyasta cewa waɗannan ayyuka za su samar da fiye da ayyukan yi 250,000 a faɗin ƙasar.

 

Idris ya ƙara da cewa an farfaɗo da Tashar Wutar Lantarki ta Kaduna mai ƙarfin megawat 255, ana ci gaba da aikin iskar gas na AKK, tare da bunƙasa haƙo mai a yankin Kolmani (a Bauchi da Gombe).

 

Ya ce naɗin muƙaman da Shugaban Ƙasa Tinubu ya yi ya nuna haɗin kai, yana mai jaddada cewa abin da ke jagorantar shi shi ne ƙwarewa da kuma haɗin kan ƙasa.

 

Idris ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya da cewa Shirin Sabunta Fata zai ci gaba da tabbatar da daidaito a cigaban ƙasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministan Kasar Pakistan: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Hangen Nesa

Next Post

Antonio Guterres: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata

Related

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa
Kasashen Ketare

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa

6 hours ago
Tinubu
Manyan Labarai

APC Da PDP Na Zargin Juna Kan Amfani Da Addini Wajen Neman Nasara A 2027

7 hours ago
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban
Manyan Labarai

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban Ƙasa

7 hours ago
Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri
Manyan Labarai

Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri

8 hours ago
SERAP, Amnesty Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Sowore, X Da Facebook
Manyan Labarai

SERAP, Amnesty Sun Bukaci Tinubu Ya Janye Ƙarar Da Ya Shigar Kan Sowore, X Da Facebook

12 hours ago
Komai Nisan Dare Gari Zai Waye
Ra'ayi Riga

Komai Nisan Dare Gari Zai Waye

13 hours ago
Next Post
Antonio Guterres: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata

Antonio Guterres: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata

LABARAI MASU NASABA

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa

Birtaniya Ta Amince Da Kafa Falasɗin A Matsayin Ƙasa

September 21, 2025
Tinubu

APC Da PDP Na Zargin Juna Kan Amfani Da Addini Wajen Neman Nasara A 2027

September 21, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban Ƙasa

September 21, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Tawagar Membobin Majalisar Wakilai Ta Amurka

Li Qiang Ya Gana Da Tawagar Membobin Majalisar Wakilai Ta Amurka

September 21, 2025
Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri

Bayan Nesanta Kanta, Jami’ar European American Ta Yi Wa Rarara Tayin Digiri

September 21, 2025
Masana Sun Yaba Da Shawarar GGI Da Kasar Sin Ta Gabatar A Taron Kara Wa Juna Sani Na CMG 

Masana Sun Yaba Da Shawarar GGI Da Kasar Sin Ta Gabatar A Taron Kara Wa Juna Sani Na CMG 

September 21, 2025
arewa

Lokaci Yayi Da Shugabannin Arewa Za Su Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Yankin –  ACI

September 21, 2025
Yadda Wasu Mata Ke Gwada Mazansu Ta Hanyar Magana Da Su Ta Wasu Hanyoyi Don Sanin Ku Suna Kula Mata

Yadda Wasu Mata Ke Gwada Mazansu Ta Hanyar Magana Da Su Ta Wasu Hanyoyi Don Sanin Ku Suna Kula Mata

September 21, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Hau Turbar Hadin Gwiwa Da Samun Moriyar Juna A Sabon Lokaci

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Hau Turbar Hadin Gwiwa Da Samun Moriyar Juna A Sabon Lokaci

September 21, 2025
Tinubu

Mata Ne Ƙashin Bayan Gyaran Duk Wata Al’umma, In Ji  Sheik Shamsudeen

September 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.