• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Yi Daidai Da Ya Zabi Musulmi Mataimaki – Oshiomhole

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Tinubu

Tikitin Kirista Da Musulmi Ba Zai Kai Mu Ga Nasara Ba, Tinubu Ya Yi Daidai Na Zabin Musulmi, Inji Tsohon Shugaban APC, Oshiomhole

Tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na kasa kuma tsohon gwamnan Jihar Edo, Adams Oshiomhole, ya sanya kafa ya shure sukar da wasu ke ta yi ga zabin Musulmi da dan takarar shugaban Shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ya yi a matsayin abokin takararsa.

  • Mataimaki: Gwamnonin APC Na Alfahari Da Zabin Tinubu – Bagudu

Oshiomhole ya ce, lokaci ya yi da za a cire wani kabilanci ko addinanci a maida hankali wajen zabin wadanda suka dace domin ceto Nijeriya daga halin da take ciki.

Adams wanda ke ganawa da TVC ya nuna gamsuwarsa da tikitin Musulmi da Musulmi da APC ta yi, ya kara da jinjina wa Tinubu bisa daukan wannan kyakkyawar matakin na zabin tsohon gwamnan Jihar Borno, Sanata Kashim Shettima a matsayin abokin takararsa.

Ya ce, “Wasu jam’iyyun adawa ma suna tsoma bakinsu kan muhawarar tikitin musulmai biyu, amma ni kam na gamsu da matakin da Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya dauka.”

LABARAI MASU NASABA

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Oshiomhole ya gamsu da zabin Shettima ne bisa dacewa da cancantar sa gami da irin nasarorin da ya cimma a baya, “Bai kamata ya zama kamar al’ada ba. Na gamsu da nagartar Shettima. Kuma nasarorin da ya cimma a rayuwarsa tabbas zai tabuka abun a zo a gani a matsayin matakin Shugaban kasa.”

Ya kara da cewa, kyawawan tarihin da Shettima ke da shi, zai yi kara wa APC tagomashi a zaben 2023, kuma ba ma maganar kirista ko Musulmi ya dace a maida hankali a APC ba, inda ya ce, “Wadanda za su iya kawo wa jam’iyyar nasara ya kamata a fi la’akari da su. Don haka wannan matakin shine daidai muddin nasara ake nema.”

Dangane da masu cewa ana neman karfafan addini ne a lamarin, Tsohon Shugaban APCn ya ce Tinubu ko a gidansa ma bai addinantar da kowa ba, “Don haka ba wani abu na damuwa a wannan lamarin. Sun ce ana kokarin maida lamarin na addini, to Tinubu ko iyalansa bai iya addinantar da su ba. Ko kun ga ya addinantar da iyalansa? Matarsa kirista ce kuma Fasto.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson
Manyan Labarai

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Next Post
Kamata Ya Yi A Hukunta ‘Yan Siyasar Amurka Da Suka Kitsa Juyin Mulki A Wasu Kasashe

Kamata Ya Yi A Hukunta ‘Yan Siyasar Amurka Da Suka Kitsa Juyin Mulki A Wasu Kasashe

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

October 16, 2025
Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025
Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

October 15, 2025
Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

October 15, 2025
Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

October 15, 2025
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

October 15, 2025
Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

October 15, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

October 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.