ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Yi Daidai Da Ya Zabi Musulmi Mataimaki – Oshiomhole

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Tinubu

Tikitin Kirista Da Musulmi Ba Zai Kai Mu Ga Nasara Ba, Tinubu Ya Yi Daidai Na Zabin Musulmi, Inji Tsohon Shugaban APC, Oshiomhole

Tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na kasa kuma tsohon gwamnan Jihar Edo, Adams Oshiomhole, ya sanya kafa ya shure sukar da wasu ke ta yi ga zabin Musulmi da dan takarar shugaban Shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ya yi a matsayin abokin takararsa.

  • Mataimaki: Gwamnonin APC Na Alfahari Da Zabin Tinubu – Bagudu

Oshiomhole ya ce, lokaci ya yi da za a cire wani kabilanci ko addinanci a maida hankali wajen zabin wadanda suka dace domin ceto Nijeriya daga halin da take ciki.

ADVERTISEMENT

Adams wanda ke ganawa da TVC ya nuna gamsuwarsa da tikitin Musulmi da Musulmi da APC ta yi, ya kara da jinjina wa Tinubu bisa daukan wannan kyakkyawar matakin na zabin tsohon gwamnan Jihar Borno, Sanata Kashim Shettima a matsayin abokin takararsa.

Ya ce, “Wasu jam’iyyun adawa ma suna tsoma bakinsu kan muhawarar tikitin musulmai biyu, amma ni kam na gamsu da matakin da Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya dauka.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

Oshiomhole ya gamsu da zabin Shettima ne bisa dacewa da cancantar sa gami da irin nasarorin da ya cimma a baya, “Bai kamata ya zama kamar al’ada ba. Na gamsu da nagartar Shettima. Kuma nasarorin da ya cimma a rayuwarsa tabbas zai tabuka abun a zo a gani a matsayin matakin Shugaban kasa.”

Ya kara da cewa, kyawawan tarihin da Shettima ke da shi, zai yi kara wa APC tagomashi a zaben 2023, kuma ba ma maganar kirista ko Musulmi ya dace a maida hankali a APC ba, inda ya ce, “Wadanda za su iya kawo wa jam’iyyar nasara ya kamata a fi la’akari da su. Don haka wannan matakin shine daidai muddin nasara ake nema.”

Dangane da masu cewa ana neman karfafan addini ne a lamarin, Tsohon Shugaban APCn ya ce Tinubu ko a gidansa ma bai addinantar da kowa ba, “Don haka ba wani abu na damuwa a wannan lamarin. Sun ce ana kokarin maida lamarin na addini, to Tinubu ko iyalansa bai iya addinantar da su ba. Ko kun ga ya addinantar da iyalansa? Matarsa kirista ce kuma Fasto.”

Tinubu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Tinubu
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
Kamata Ya Yi A Hukunta ‘Yan Siyasar Amurka Da Suka Kitsa Juyin Mulki A Wasu Kasashe

Kamata Ya Yi A Hukunta ‘Yan Siyasar Amurka Da Suka Kitsa Juyin Mulki A Wasu Kasashe

LABARAI MASU NASABA

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

’Yan Takarar ADC A Arewa Maso Yamma Sun Yi Alƙawarin Biyan N110,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

September 9, 2026
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.