• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Trump Ya Sha Alwashin Fatattakar Baki Daga Amurka Idan Aka Sake Zaben Sa

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
10 months ago
in Labarai
0
trump
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Donald Trump ya kara jaddada matsayarsa a kan kwararar baki cikin Amurka, inda ya sha alwashin aiwatar da manufarsa ta fatattakar baki ”mafi girma a tarihi”, idan ya sake zama shugaban kasa.

 

A hirar da ya yi kai tsaye da shugaban shafin sada zumunta na D, Elon Musk, Mr Trump ya yi karin haske kan matsayar sa game da baki masu shiga Amurka ba bisa ka’ida ba, da kuma yunkurin kashe shi da aka yi.

  • Shugaban Seychelles: Raya Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Na Da Makoma Mai Haske
  • Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu

An dan samu tsaiko kafin fara tattaunawar da dinbin jama’a suka yi ta jira domin sauraro a shafin X.

 

Labarai Masu Nasaba

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Shi dai Mr Elon Musk ya alakanta jinkirin da aka samu ne da yunkurin yin kutse da ya ce wasu sun rika yi cikin shafin, a daidai lokacin da ake shirin fara tattaunawar.

 

Dan takarar shugabancin Amurkan a jam’iyyar Republican, ya shaidawa hamshakin attajirin cewa ba zai yi wata-wata ba, wajen zartar da korar baki mafi girma a tarihi, idan har ya lashe zaben shugaban kasa a watan Nuwamba mai zuwa.

 

Mr Trump ya ce ba gudu babu ja da baya a shirin sa na gina katangar da za ta zamo shinge domin kare kasarsa daga kwararar bakin da za su zame mata barazana.

 

Ya ce: “Aikata laifi ya ragu a duniya baki daya, kuma ka jira tukun sai ka ga alkalumman da muke da su.

 

Wannan babban laifi ne, shiga kasa ba bisa ka’ida ba. Ya kara da cewa ”Mutane ne abin tsoro. Mutane ne da aka tura gidan yari saboda aikata kisan kai da sauran manyan laifuka, kuma sun zo suna turo mana su cikin kasarmu, suna kuma gargadin su cewa idan har suka koma za a kashe su.

 

Ko dai za a yanke masu hukuncin kisa ko kuma a kashe su nan take, idan har suka koma kasashen nasu. Wadan nan fa masu laifi ne da tsananin laifinsu ya sa muke kallon namu masu laifin kamar ba masu laifi ba, abin da suke aikatawa ya yi muni sosai.’’

 

An dai yi wannan tattaunawa ce bayan abokiyar hamayyar Donald Trump, Kamala Harris, ta shige gabansa a kuri’ar jin ra’ayin jama’a.

 

Mr Musk ya fito fili ya bayyana goyon bayansa ga Mr Trump ne bayan an yi yunkurin kashe tsohon shugaban Amurkan a wajen yakin neman zabe a watan jiya.

 

A ranar Litinin Donald Trump ya koma amfani da shafin D, a karon farko cikin kusan shekara guda, kuma ya wallafa sakonni bidiyo na neman zabensa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar Nijeriya da TuraiAmurkaEU
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dasuki Ya Kaddamar Da Shirin Tallafa Wa Masu Kananan Sana’o’i Da Manoma

Next Post

Mutum 68 Sun Mutu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Sudan

Related

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

31 minutes ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

4 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

7 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

7 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

17 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

19 hours ago
Next Post
Mutum 68 Sun Mutu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Sudan

Mutum 68 Sun Mutu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Sudan

LABARAI MASU NASABA

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.