• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Trump Ya Sha Alwashin Fatattakar Baki Daga Amurka Idan Aka Sake Zaben Sa

by Sulaiman and Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
trump
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Donald Trump ya kara jaddada matsayarsa a kan kwararar baki cikin Amurka, inda ya sha alwashin aiwatar da manufarsa ta fatattakar baki ”mafi girma a tarihi”, idan ya sake zama shugaban kasa.

 

A hirar da ya yi kai tsaye da shugaban shafin sada zumunta na D, Elon Musk, Mr Trump ya yi karin haske kan matsayar sa game da baki masu shiga Amurka ba bisa ka’ida ba, da kuma yunkurin kashe shi da aka yi.

  • Shugaban Seychelles: Raya Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Na Da Makoma Mai Haske
  • Nazari Kan Dabarun Koyarwa Da Amfaninsu

An dan samu tsaiko kafin fara tattaunawar da dinbin jama’a suka yi ta jira domin sauraro a shafin X.

 

Labarai Masu Nasaba

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Shi dai Mr Elon Musk ya alakanta jinkirin da aka samu ne da yunkurin yin kutse da ya ce wasu sun rika yi cikin shafin, a daidai lokacin da ake shirin fara tattaunawar.

 

Dan takarar shugabancin Amurkan a jam’iyyar Republican, ya shaidawa hamshakin attajirin cewa ba zai yi wata-wata ba, wajen zartar da korar baki mafi girma a tarihi, idan har ya lashe zaben shugaban kasa a watan Nuwamba mai zuwa.

 

Mr Trump ya ce ba gudu babu ja da baya a shirin sa na gina katangar da za ta zamo shinge domin kare kasarsa daga kwararar bakin da za su zame mata barazana.

 

Ya ce: “Aikata laifi ya ragu a duniya baki daya, kuma ka jira tukun sai ka ga alkalumman da muke da su.

 

Wannan babban laifi ne, shiga kasa ba bisa ka’ida ba. Ya kara da cewa ”Mutane ne abin tsoro. Mutane ne da aka tura gidan yari saboda aikata kisan kai da sauran manyan laifuka, kuma sun zo suna turo mana su cikin kasarmu, suna kuma gargadin su cewa idan har suka koma za a kashe su.

 

Ko dai za a yanke masu hukuncin kisa ko kuma a kashe su nan take, idan har suka koma kasashen nasu. Wadan nan fa masu laifi ne da tsananin laifinsu ya sa muke kallon namu masu laifin kamar ba masu laifi ba, abin da suke aikatawa ya yi muni sosai.’’

 

An dai yi wannan tattaunawa ce bayan abokiyar hamayyar Donald Trump, Kamala Harris, ta shige gabansa a kuri’ar jin ra’ayin jama’a.

 

Mr Musk ya fito fili ya bayyana goyon bayansa ga Mr Trump ne bayan an yi yunkurin kashe tsohon shugaban Amurkan a wajen yakin neman zabe a watan jiya.

 

A ranar Litinin Donald Trump ya koma amfani da shafin D, a karon farko cikin kusan shekara guda, kuma ya wallafa sakonni bidiyo na neman zabensa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Alakar Nijeriya da TuraiAmurkaEU
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dasuki Ya Kaddamar Da Shirin Tallafa Wa Masu Kananan Sana’o’i Da Manoma

Next Post

Mutum 68 Sun Mutu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Sudan

Related

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

47 minutes ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

13 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

15 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

17 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

20 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

22 hours ago
Next Post
Mutum 68 Sun Mutu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Sudan

Mutum 68 Sun Mutu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Sudan

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.