• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Kayan Abinci: Za A Fuskanci Barazanar Yunwa A Nijeriya – Rahoto

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Tsadar Kayan Abinci: Za A Fuskanci Barazanar Yunwa A Nijeriya – Rahoto
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani rahoton da ta fitar a makon da ya gabata, hukumar samar da abinci ta duniya wato, WFP ta ce yunwa za ta tsananta a shekarar 2022 a Nijeriya sakamakon karuwar hare-haren ‘yan bindiga musamman a Arewacin kasar nan.

Bugu da kari, rahoton ya ce fiye da mutum miliyan 31 a yankin yammacin Afirka za su fuskanci barazanar yunwa sakamakon tsadar kayan abinci da kuma rikici da matsaloli na tsaro.

  • Tarayyar Turai Ta Tallafawa Nijeriya Da Kayan Abinci Na Uro Miliyan 600

A cewar rahoton farashin abinci ya ninka da sama da kashi 200 a kasashen yammacin Afirka, wanda ya jefa masu karamin karfi cikin mawuyacin hali na samun abin da za su kai baka, sakamakon matakan da annobar korona ta tilasta aka dauka na tattalin arziki.

Rashin noman zai kara haifar da karancin abinci da kuma tsadarsa, kamar yadda yin noma zai samar da abinci da rahusa.
Bisa ga alkaluman da hukumar kdiddiga ta kasa ta fitar a watan Fabarairu sun nuna cewa, an samu hauhauwar farashin da ya kai kashi 17.33 cikin dari a watan Fabrairu da ya wuce, inda kuma alkaluman suka nuna cewa tashin farashin ya karu da kashi 1.54 a watan Fabarairun 2022, idan aka kwatanta da kashi 1.49 a watan Janairu.
.
Har Ila yau, farashin kayan abinci ya tashi da kashi 21.79 a Fabarairun da ya gabata, idan aka kwatanta da kashi 20.57 a watan Janairu.

Hukumar ta ce, wannan ne karon farko da aka samu irin wannan tashin farashi a cikin shekaru hudu da suka wuce.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

Bugu da kari, a yayin da daminar bana ta kankama an kuma ci gaba da fuskantar tsadar kayan abinci da hare-haren ‘yan bindiga da satar mutane, al’amarin da ya jefa manoma a arewacin kasar nan a cikin matsala, inda musamman abin ya fi shafar manoman da ke karkara, inda matsalar ta janyo koma-baya noma da kuma kara janyo samun kudaden shiga ga manoma.

Hare-haren ‘yan bindiga da masu fashin-daji a kauyukan jihohin arewa maso yammacin kasar nan musamman Zamfara da Katsina da yankin Birnin Gwari a Kaduna sai kara munana yake yi.
Manoma da dama a wadannan jihohin, tuni suka hakura da manyan gonakinsu da ke a kauyukansu inda suke ci gaba da jin tsoron koma wa don su ci gaba da yin noman.

Rashin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali musamman a jihohin Arewa maso yammacin kasar nan ya sa har yanzu manoman da suka yi gudun hijira ba su koma gonakinsu ba, matakin da ya rage yawan abincin da ake samarwa a kasar nan.

Wasu manoma ‘yan gudun hijira daga jihar Zamfara sun bayyana cewa kafin su yi gudu hijira suna noma sosai wanda suke ciyar da iyalinsu har su kai kasuwa su sayar, amma yanzu ba sa da halin yin noman.

A cewarsu, ‘yan fashin-daji sun hana su sakat, inda hakan ya tilasata suke arece wa don su tsira da rayukansu, inda suka bayyana cewa za a shafe shekaru goma a jihar kafin noma ya dawo daidai saboda a cewarsa noman gaske da aka sani a Zamfara ya gagara, saboda hare-haren ‘yan bindiga.

Wasu masana a fannin aikin noma a kasar nan sun yi hasashen cewa, zai yi wuya a noma amfanin gonar da aka saba samu nan da sama da shekaru goma masu zuwa, musamman a jihohin da matsalar ta fi ta’azzara, in har makunta a kasar nan, ba su gaggauta lalubo da mafita ba.

Har ila yau, masanan sun yi nuni da cewa, rashin tsaro da kwanciyar hankali ga manoman wata babbar barazana ce ga wadatar abinci a kasar nan, musamman a arewacin kasar nan.

Sun sanar da cewa, hauhawar farashin kayayyaki masarufi a kasar nan na ci gaba da yi wa tattalin arziki Nijeriya illa haka wasu masana a fannin arzikin tattalin arzikin kasar nan, inda kuma faduwar darajar naira,
Matsalar tsaro na daga cikin abubuwan da ake hasashen za su haddasa karancin abinci a arewacin Nijeriya saboda yadda ‘yan fashin-daji da masu garkuwa ke addabar manoma suna hana su nome gonakinsu.

Ana ganin kalunbalen tsaro da manoma ke fuskanta zai yi tasiri ga samar da abinci a Nijeriya.

Masanan sun kara da cewa misalia wasu yankunan Katsina suna noma abinci kusan kashi 30 zuwa 35 na abin da ake samu a arewa maso yamma gaba daya, sai dai a yanzu noman zai gagara, manoma za su kasa zuwa gona, inda suka bayyana cewa, wannan matsala suka ce za ta haifar da tsadar kayayyakin abinci a yankin arewacin Nijeriya saboda rashin abincin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gano Wata Kabila Da Take Bauta Wa Talotalo

Next Post

Muhammad Abacha Ne Dan Takarar PDP A Kano- INEC

Related

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

4 days ago
Gwamnonin Arewa Na Kokarin Farfado Da Hadin Kan Yankin
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi

4 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni

4 days ago
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci A Sama Wa Manoma Masu Renon Tsirrai Rancen Kudi

2 weeks ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Zuba Dala Biliyan 74 A Fannin Kiwon Dabbobi

2 weeks ago
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

3 weeks ago
Next Post
Muhammad Abacha Ne Dan Takarar PDP A Kano- INEC

Muhammad Abacha Ne Dan Takarar PDP A Kano- INEC

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

June 4, 2025
DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.