• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Kayan Abinci: Za A Fuskanci Barazanar Yunwa A Nijeriya – Rahoto

by Abubakar Abba
3 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Tsadar Kayan Abinci: Za A Fuskanci Barazanar Yunwa A Nijeriya – Rahoto
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani rahoton da ta fitar a makon da ya gabata, hukumar samar da abinci ta duniya wato, WFP ta ce yunwa za ta tsananta a shekarar 2022 a Nijeriya sakamakon karuwar hare-haren ‘yan bindiga musamman a Arewacin kasar nan.

Bugu da kari, rahoton ya ce fiye da mutum miliyan 31 a yankin yammacin Afirka za su fuskanci barazanar yunwa sakamakon tsadar kayan abinci da kuma rikici da matsaloli na tsaro.

  • Tarayyar Turai Ta Tallafawa Nijeriya Da Kayan Abinci Na Uro Miliyan 600

A cewar rahoton farashin abinci ya ninka da sama da kashi 200 a kasashen yammacin Afirka, wanda ya jefa masu karamin karfi cikin mawuyacin hali na samun abin da za su kai baka, sakamakon matakan da annobar korona ta tilasta aka dauka na tattalin arziki.

Rashin noman zai kara haifar da karancin abinci da kuma tsadarsa, kamar yadda yin noma zai samar da abinci da rahusa.
Bisa ga alkaluman da hukumar kdiddiga ta kasa ta fitar a watan Fabarairu sun nuna cewa, an samu hauhauwar farashin da ya kai kashi 17.33 cikin dari a watan Fabrairu da ya wuce, inda kuma alkaluman suka nuna cewa tashin farashin ya karu da kashi 1.54 a watan Fabarairun 2022, idan aka kwatanta da kashi 1.49 a watan Janairu.
.
Har Ila yau, farashin kayan abinci ya tashi da kashi 21.79 a Fabarairun da ya gabata, idan aka kwatanta da kashi 20.57 a watan Janairu.

Hukumar ta ce, wannan ne karon farko da aka samu irin wannan tashin farashi a cikin shekaru hudu da suka wuce.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Bugu da kari, a yayin da daminar bana ta kankama an kuma ci gaba da fuskantar tsadar kayan abinci da hare-haren ‘yan bindiga da satar mutane, al’amarin da ya jefa manoma a arewacin kasar nan a cikin matsala, inda musamman abin ya fi shafar manoman da ke karkara, inda matsalar ta janyo koma-baya noma da kuma kara janyo samun kudaden shiga ga manoma.

Hare-haren ‘yan bindiga da masu fashin-daji a kauyukan jihohin arewa maso yammacin kasar nan musamman Zamfara da Katsina da yankin Birnin Gwari a Kaduna sai kara munana yake yi.
Manoma da dama a wadannan jihohin, tuni suka hakura da manyan gonakinsu da ke a kauyukansu inda suke ci gaba da jin tsoron koma wa don su ci gaba da yin noman.

Rashin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali musamman a jihohin Arewa maso yammacin kasar nan ya sa har yanzu manoman da suka yi gudun hijira ba su koma gonakinsu ba, matakin da ya rage yawan abincin da ake samarwa a kasar nan.

Wasu manoma ‘yan gudun hijira daga jihar Zamfara sun bayyana cewa kafin su yi gudu hijira suna noma sosai wanda suke ciyar da iyalinsu har su kai kasuwa su sayar, amma yanzu ba sa da halin yin noman.

A cewarsu, ‘yan fashin-daji sun hana su sakat, inda hakan ya tilasata suke arece wa don su tsira da rayukansu, inda suka bayyana cewa za a shafe shekaru goma a jihar kafin noma ya dawo daidai saboda a cewarsa noman gaske da aka sani a Zamfara ya gagara, saboda hare-haren ‘yan bindiga.

Wasu masana a fannin aikin noma a kasar nan sun yi hasashen cewa, zai yi wuya a noma amfanin gonar da aka saba samu nan da sama da shekaru goma masu zuwa, musamman a jihohin da matsalar ta fi ta’azzara, in har makunta a kasar nan, ba su gaggauta lalubo da mafita ba.

Har ila yau, masanan sun yi nuni da cewa, rashin tsaro da kwanciyar hankali ga manoman wata babbar barazana ce ga wadatar abinci a kasar nan, musamman a arewacin kasar nan.

Sun sanar da cewa, hauhawar farashin kayayyaki masarufi a kasar nan na ci gaba da yi wa tattalin arziki Nijeriya illa haka wasu masana a fannin arzikin tattalin arzikin kasar nan, inda kuma faduwar darajar naira,
Matsalar tsaro na daga cikin abubuwan da ake hasashen za su haddasa karancin abinci a arewacin Nijeriya saboda yadda ‘yan fashin-daji da masu garkuwa ke addabar manoma suna hana su nome gonakinsu.

Ana ganin kalunbalen tsaro da manoma ke fuskanta zai yi tasiri ga samar da abinci a Nijeriya.

Masanan sun kara da cewa misalia wasu yankunan Katsina suna noma abinci kusan kashi 30 zuwa 35 na abin da ake samu a arewa maso yamma gaba daya, sai dai a yanzu noman zai gagara, manoma za su kasa zuwa gona, inda suka bayyana cewa, wannan matsala suka ce za ta haifar da tsadar kayayyakin abinci a yankin arewacin Nijeriya saboda rashin abincin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gano Wata Kabila Da Take Bauta Wa Talotalo

Next Post

Muhammad Abacha Ne Dan Takarar PDP A Kano- INEC

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

4 days ago
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

5 days ago
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
Noma Da Kiwo

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

5 days ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

6 days ago
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

2 weeks ago
Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
Noma Da Kiwo

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

2 weeks ago
Next Post
Muhammad Abacha Ne Dan Takarar PDP A Kano- INEC

Muhammad Abacha Ne Dan Takarar PDP A Kano- INEC

LABARAI MASU NASABA

Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don YaÆ™ar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.