Shugaba Bola Tinubu na duba yiwuwar dawo da bayar da tallafin man fetur na dan wucin gadi biyo bayan matsin rayuwa da aka shiga da kuma yadda farashin Dalar Amurka ke ta hauhawa tun bayan cire tallafin a watan Mayu, Inji jaridar TheCable
Har yanzu dai shugaban bai tabbatar da wannan kuduri ba amma takardar shawarar tana kan teburinsa, kamar yadda wata majiya daga fadar shugaban kasa ta shaidawa TheCable.
Tuni dai kungiyoyin kwadago suka yi barazanar shiga yajin aiki na sai Baba-ta-gani idan farashin man fetur ya kara hauhawa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp