• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin BRICS Ya Zama Dandalin Kare Moriyar Kasashe Masu Tasowa

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Tsarin BRICS Ya Zama Dandalin Kare Moriyar Kasashe Masu Tasowa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Taron kolin BRICS da ya gudana a kasar Afrika ta Kudu a kwanakin nan ya gabatar da wasu salon musamman na Afirka. Da farko, kasar Afrika ta Kudu ce ta dauki nauyin karbar bakuncin taron. Na biyu, cikin manyan kusoshi fiye da 60 da aka gayyata don halartar taron, a kalla akwai manyan jami’ai 30 wadanda suka zo daga kasashen Afirka. Na uku, cikin kasashe 6 da aka gayyace su don su zama mambobin tsarin BRICS a wannan karo, akwai wasu kasashe 2 dake cikin nahiyar Afirka, wato Masar, da Habasha.

Ban yi mamaki ba kan yadda taron BRICS ya nuna yanayi mai alaka da nahiyar Afirka, saboda nahiyar ta kunshi mafi yawan kasashe masu tasowa. Yayin da tsarin hadin gwiwa na BRICS ya riga ya zama wani muhimmin dandali ga kasashe masu tasowa, don su karfafa hadin gwiwa, tare da kare moriyarsu ta bai daya.

  • Xi Jinping: Za Kara Karfin Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Me ya sa ake bukatar wani nau’in dandali kamar haka? Saboda yayin da tattalin arzikin duniya ke fama da yanayi na koma baya, kana rikice-rikice na ci gaba da kasancewa a wasu yankuna, tsare-tsaren kasa da kasa a fannonin tattalin arziki da siyasa da kasashen yamma ke jagoranta, na kara karkata ga moriyar kasashen yamma ne, maimakon ba da kulawa ga kasashe masu tasowa.

Alal misali, da yawa daga cikin shugabannin kasashen Afirka sun bayyana cewa, matsayin dalar Amurka mai muhimmanci ya hana tattalin arzikin kasashensu ci gaba. Saboda yadda kasar Amurka ke kara kudin ruwan ajiya a kai a kai ya haddasa hauhawar darajar kudin kasar, wanda ke sanya sauran kasashe kashe kudi fiye da kima don shigar da kayayyaki daga ketare, gami da karuwar yawan basusukan da ake binsu. Game da matsalolin da karuwar darajar dalar Amurka ke haddasa wa tattalin arzikin sauran kasashe, na san abokanmu dake Najeriya sun fahimce su sosai.

Sa’an nan a fannin harkar siyasar kasa da kasa, kasar Amurka da kawayenta na yammacin duniya sun sa hannu cikin rikicin dake tsakanin Rasha da Ukraine, inda suke ba da taimako ga wani bangare, gami da tilastawa sauran kasashe bin sahunsu. Sai dai kasashen Afirka suna son ci gaba da hadin gwiwa da kasar Rasha, da neman ganin an kawo karshen yakin da ake yi cikin sauri, kuma ta hanyar lumana, bisa la’akari da moriya kansu.

Labarai Masu Nasaba

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

A sa’i daya, kasashen Afirka da kasashe masu tasowa na sauran yankuna suna son ganin gyare-gyare kan tsare-tsaren bankin duniya, da hukumar ba da lamuni ta duniya, da kasashen yamma suka kafa, don magance samar da karin tallafi ga kasashe masu sukuni, maimakon kula da kasashe marasa karfi. Wadannan abubuwan da na ambata suna cikin cece-kuce da ake samu tsakanin kasashe masu tasowa, da kasashen yamma, sakamakon bambancin moriyar su.

Saboda haka, yadda tsarin BRICS yake habaka, da yadda yake sa kaimi ga yin kwaskwarima kan tsarin hada-hadar kudi na duniya, sun yi daidai da bukatun dimbin kasashe masu tasowa. Inda a ganinsu, ci gaban da tsarin BRICS ya samu ya nuna yadda kasashe masu tasowa ke samun karin ikon fada a ji a duniya, da karin damammaki na tabbatar da moriyarsu. Batun nan ya yi kama da maganar da shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya fada a wajen taron kolin BRICS na wannan karo, inda ya ce, ya kamata kasashen BRICS su haifar da sauyin yanayi ga tsarin kula da duniya, don neman tabbatar da adalci da kima, da wani yanayi na tabbas, da karko, gami da ci gaba.

Idan karin kasashe masu tasowa sun karfafa hadin gwiwarsu ta hanyar tsarin BRICS, to, za su samu isashen karfin yin garambawul kan tsare-tsaren duniya. Saboda ko kasashe mambobi guda 5 da suke cikin tsarin a halin yanzu, wato Brazil, da Rasha, da Indiya, da Sin, da Afirka ta Kudu, sun riga sun dauki kaso 24.3 na tattalin arzikin duniya, da kaso 26.46 na fadin harabar kasashen duniya, gami da kaso 43 na daukacin al’ummar duniya. Yayin da ake sa ran ganin karuwar wadannan adadi a kai a kai a nan gaba. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kashe ‘Yan Ta’adda 41 Yayin Da Boko Haram Da ISWAP Suka Bai Wa Hammata Isla A Borno

Next Post

Shugaba Xi Jinping Da Takwaransa Na Afirka Ta Kudu Sun Jagoranci Taron Tattaunawa A Tsakanin Shugabannin Sin Da Afirka

Related

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”
Daga Birnin Sin

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

15 minutes ago
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

2 hours ago
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157
Daga Birnin Sin

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

4 hours ago
Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 
Daga Birnin Sin

Za A Bude Cibiyar Watsa Labarai Game Da Bukukuwan Nasarar Yaki Da Harin Japan 

22 hours ago
An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Makon Fina-finai Da Shirye-shiryen Talabijin Na SCO A Qingdao

23 hours ago
CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 
Daga Birnin Sin

CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Faretin Soja Na Beijing Cikin Harsuna 85 Ga Duk Fadin Duniya 

1 day ago
Next Post
Shugaba Xi Jinping Da Takwaransa Na Afirka Ta Kudu Sun Jagoranci Taron Tattaunawa A Tsakanin Shugabannin Sin Da Afirka

Shugaba Xi Jinping Da Takwaransa Na Afirka Ta Kudu Sun Jagoranci Taron Tattaunawa A Tsakanin Shugabannin Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

August 25, 2025
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

August 25, 2025
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

August 25, 2025
Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

August 25, 2025
Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

Ƙungiyar KSCI Ta Nemi Sabon Tsari Don Magance Ƴan Bindiga A Katsina

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.