• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin BRICS Ya Zama Dandalin Kare Moriyar Kasashe Masu Tasowa

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Tsarin BRICS Ya Zama Dandalin Kare Moriyar Kasashe Masu Tasowa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Taron kolin BRICS da ya gudana a kasar Afrika ta Kudu a kwanakin nan ya gabatar da wasu salon musamman na Afirka. Da farko, kasar Afrika ta Kudu ce ta dauki nauyin karbar bakuncin taron. Na biyu, cikin manyan kusoshi fiye da 60 da aka gayyata don halartar taron, a kalla akwai manyan jami’ai 30 wadanda suka zo daga kasashen Afirka. Na uku, cikin kasashe 6 da aka gayyace su don su zama mambobin tsarin BRICS a wannan karo, akwai wasu kasashe 2 dake cikin nahiyar Afirka, wato Masar, da Habasha.

Ban yi mamaki ba kan yadda taron BRICS ya nuna yanayi mai alaka da nahiyar Afirka, saboda nahiyar ta kunshi mafi yawan kasashe masu tasowa. Yayin da tsarin hadin gwiwa na BRICS ya riga ya zama wani muhimmin dandali ga kasashe masu tasowa, don su karfafa hadin gwiwa, tare da kare moriyarsu ta bai daya.

  • Xi Jinping: Za Kara Karfin Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Me ya sa ake bukatar wani nau’in dandali kamar haka? Saboda yayin da tattalin arzikin duniya ke fama da yanayi na koma baya, kana rikice-rikice na ci gaba da kasancewa a wasu yankuna, tsare-tsaren kasa da kasa a fannonin tattalin arziki da siyasa da kasashen yamma ke jagoranta, na kara karkata ga moriyar kasashen yamma ne, maimakon ba da kulawa ga kasashe masu tasowa.

Alal misali, da yawa daga cikin shugabannin kasashen Afirka sun bayyana cewa, matsayin dalar Amurka mai muhimmanci ya hana tattalin arzikin kasashensu ci gaba. Saboda yadda kasar Amurka ke kara kudin ruwan ajiya a kai a kai ya haddasa hauhawar darajar kudin kasar, wanda ke sanya sauran kasashe kashe kudi fiye da kima don shigar da kayayyaki daga ketare, gami da karuwar yawan basusukan da ake binsu. Game da matsalolin da karuwar darajar dalar Amurka ke haddasa wa tattalin arzikin sauran kasashe, na san abokanmu dake Najeriya sun fahimce su sosai.

Sa’an nan a fannin harkar siyasar kasa da kasa, kasar Amurka da kawayenta na yammacin duniya sun sa hannu cikin rikicin dake tsakanin Rasha da Ukraine, inda suke ba da taimako ga wani bangare, gami da tilastawa sauran kasashe bin sahunsu. Sai dai kasashen Afirka suna son ci gaba da hadin gwiwa da kasar Rasha, da neman ganin an kawo karshen yakin da ake yi cikin sauri, kuma ta hanyar lumana, bisa la’akari da moriya kansu.

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

A sa’i daya, kasashen Afirka da kasashe masu tasowa na sauran yankuna suna son ganin gyare-gyare kan tsare-tsaren bankin duniya, da hukumar ba da lamuni ta duniya, da kasashen yamma suka kafa, don magance samar da karin tallafi ga kasashe masu sukuni, maimakon kula da kasashe marasa karfi. Wadannan abubuwan da na ambata suna cikin cece-kuce da ake samu tsakanin kasashe masu tasowa, da kasashen yamma, sakamakon bambancin moriyar su.

Saboda haka, yadda tsarin BRICS yake habaka, da yadda yake sa kaimi ga yin kwaskwarima kan tsarin hada-hadar kudi na duniya, sun yi daidai da bukatun dimbin kasashe masu tasowa. Inda a ganinsu, ci gaban da tsarin BRICS ya samu ya nuna yadda kasashe masu tasowa ke samun karin ikon fada a ji a duniya, da karin damammaki na tabbatar da moriyarsu. Batun nan ya yi kama da maganar da shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya fada a wajen taron kolin BRICS na wannan karo, inda ya ce, ya kamata kasashen BRICS su haifar da sauyin yanayi ga tsarin kula da duniya, don neman tabbatar da adalci da kima, da wani yanayi na tabbas, da karko, gami da ci gaba.

Idan karin kasashe masu tasowa sun karfafa hadin gwiwarsu ta hanyar tsarin BRICS, to, za su samu isashen karfin yin garambawul kan tsare-tsaren duniya. Saboda ko kasashe mambobi guda 5 da suke cikin tsarin a halin yanzu, wato Brazil, da Rasha, da Indiya, da Sin, da Afirka ta Kudu, sun riga sun dauki kaso 24.3 na tattalin arzikin duniya, da kaso 26.46 na fadin harabar kasashen duniya, gami da kaso 43 na daukacin al’ummar duniya. Yayin da ake sa ran ganin karuwar wadannan adadi a kai a kai a nan gaba. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kashe ‘Yan Ta’adda 41 Yayin Da Boko Haram Da ISWAP Suka Bai Wa Hammata Isla A Borno

Next Post

Shugaba Xi Jinping Da Takwaransa Na Afirka Ta Kudu Sun Jagoranci Taron Tattaunawa A Tsakanin Shugabannin Sin Da Afirka

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

2 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

4 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

4 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

8 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

9 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

10 hours ago
Next Post
Shugaba Xi Jinping Da Takwaransa Na Afirka Ta Kudu Sun Jagoranci Taron Tattaunawa A Tsakanin Shugabannin Sin Da Afirka

Shugaba Xi Jinping Da Takwaransa Na Afirka Ta Kudu Sun Jagoranci Taron Tattaunawa A Tsakanin Shugabannin Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.