ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin BRICS Ya Zama Dandalin Kare Moriyar Kasashe Masu Tasowa

by CMG Hausa
3 years ago
BRICS

Taron kolin BRICS da ya gudana a kasar Afrika ta Kudu a kwanakin nan ya gabatar da wasu salon musamman na Afirka. Da farko, kasar Afrika ta Kudu ce ta dauki nauyin karbar bakuncin taron. Na biyu, cikin manyan kusoshi fiye da 60 da aka gayyata don halartar taron, a kalla akwai manyan jami’ai 30 wadanda suka zo daga kasashen Afirka. Na uku, cikin kasashe 6 da aka gayyace su don su zama mambobin tsarin BRICS a wannan karo, akwai wasu kasashe 2 dake cikin nahiyar Afirka, wato Masar, da Habasha.

Ban yi mamaki ba kan yadda taron BRICS ya nuna yanayi mai alaka da nahiyar Afirka, saboda nahiyar ta kunshi mafi yawan kasashe masu tasowa. Yayin da tsarin hadin gwiwa na BRICS ya riga ya zama wani muhimmin dandali ga kasashe masu tasowa, don su karfafa hadin gwiwa, tare da kare moriyarsu ta bai daya.

  • Xi Jinping: Za Kara Karfin Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Me ya sa ake bukatar wani nau’in dandali kamar haka? Saboda yayin da tattalin arzikin duniya ke fama da yanayi na koma baya, kana rikice-rikice na ci gaba da kasancewa a wasu yankuna, tsare-tsaren kasa da kasa a fannonin tattalin arziki da siyasa da kasashen yamma ke jagoranta, na kara karkata ga moriyar kasashen yamma ne, maimakon ba da kulawa ga kasashe masu tasowa.

ADVERTISEMENT

Alal misali, da yawa daga cikin shugabannin kasashen Afirka sun bayyana cewa, matsayin dalar Amurka mai muhimmanci ya hana tattalin arzikin kasashensu ci gaba. Saboda yadda kasar Amurka ke kara kudin ruwan ajiya a kai a kai ya haddasa hauhawar darajar kudin kasar, wanda ke sanya sauran kasashe kashe kudi fiye da kima don shigar da kayayyaki daga ketare, gami da karuwar yawan basusukan da ake binsu. Game da matsalolin da karuwar darajar dalar Amurka ke haddasa wa tattalin arzikin sauran kasashe, na san abokanmu dake Najeriya sun fahimce su sosai.

Sa’an nan a fannin harkar siyasar kasa da kasa, kasar Amurka da kawayenta na yammacin duniya sun sa hannu cikin rikicin dake tsakanin Rasha da Ukraine, inda suke ba da taimako ga wani bangare, gami da tilastawa sauran kasashe bin sahunsu. Sai dai kasashen Afirka suna son ci gaba da hadin gwiwa da kasar Rasha, da neman ganin an kawo karshen yakin da ake yi cikin sauri, kuma ta hanyar lumana, bisa la’akari da moriya kansu.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

A sa’i daya, kasashen Afirka da kasashe masu tasowa na sauran yankuna suna son ganin gyare-gyare kan tsare-tsaren bankin duniya, da hukumar ba da lamuni ta duniya, da kasashen yamma suka kafa, don magance samar da karin tallafi ga kasashe masu sukuni, maimakon kula da kasashe marasa karfi. Wadannan abubuwan da na ambata suna cikin cece-kuce da ake samu tsakanin kasashe masu tasowa, da kasashen yamma, sakamakon bambancin moriyar su.

Saboda haka, yadda tsarin BRICS yake habaka, da yadda yake sa kaimi ga yin kwaskwarima kan tsarin hada-hadar kudi na duniya, sun yi daidai da bukatun dimbin kasashe masu tasowa. Inda a ganinsu, ci gaban da tsarin BRICS ya samu ya nuna yadda kasashe masu tasowa ke samun karin ikon fada a ji a duniya, da karin damammaki na tabbatar da moriyarsu. Batun nan ya yi kama da maganar da shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya fada a wajen taron kolin BRICS na wannan karo, inda ya ce, ya kamata kasashen BRICS su haifar da sauyin yanayi ga tsarin kula da duniya, don neman tabbatar da adalci da kima, da wani yanayi na tabbas, da karko, gami da ci gaba.

Idan karin kasashe masu tasowa sun karfafa hadin gwiwarsu ta hanyar tsarin BRICS, to, za su samu isashen karfin yin garambawul kan tsare-tsaren duniya. Saboda ko kasashe mambobi guda 5 da suke cikin tsarin a halin yanzu, wato Brazil, da Rasha, da Indiya, da Sin, da Afirka ta Kudu, sun riga sun dauki kaso 24.3 na tattalin arzikin duniya, da kaso 26.46 na fadin harabar kasashen duniya, gami da kaso 43 na daukacin al’ummar duniya. Yayin da ake sa ran ganin karuwar wadannan adadi a kai a kai a nan gaba. (Bello Wang)

BRICS
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Shugaba Xi Jinping Da Takwaransa Na Afirka Ta Kudu Sun Jagoranci Taron Tattaunawa A Tsakanin Shugabannin Sin Da Afirka

Shugaba Xi Jinping Da Takwaransa Na Afirka Ta Kudu Sun Jagoranci Taron Tattaunawa A Tsakanin Shugabannin Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.