• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin BRICS Ya Zama Dandalin Kare Moriyar Kasashe Masu Tasowa

byCMG Hausa
2 years ago
BRICS

Taron kolin BRICS da ya gudana a kasar Afrika ta Kudu a kwanakin nan ya gabatar da wasu salon musamman na Afirka. Da farko, kasar Afrika ta Kudu ce ta dauki nauyin karbar bakuncin taron. Na biyu, cikin manyan kusoshi fiye da 60 da aka gayyata don halartar taron, a kalla akwai manyan jami’ai 30 wadanda suka zo daga kasashen Afirka. Na uku, cikin kasashe 6 da aka gayyace su don su zama mambobin tsarin BRICS a wannan karo, akwai wasu kasashe 2 dake cikin nahiyar Afirka, wato Masar, da Habasha.

Ban yi mamaki ba kan yadda taron BRICS ya nuna yanayi mai alaka da nahiyar Afirka, saboda nahiyar ta kunshi mafi yawan kasashe masu tasowa. Yayin da tsarin hadin gwiwa na BRICS ya riga ya zama wani muhimmin dandali ga kasashe masu tasowa, don su karfafa hadin gwiwa, tare da kare moriyarsu ta bai daya.

  • Xi Jinping: Za Kara Karfin Wanzar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Me ya sa ake bukatar wani nau’in dandali kamar haka? Saboda yayin da tattalin arzikin duniya ke fama da yanayi na koma baya, kana rikice-rikice na ci gaba da kasancewa a wasu yankuna, tsare-tsaren kasa da kasa a fannonin tattalin arziki da siyasa da kasashen yamma ke jagoranta, na kara karkata ga moriyar kasashen yamma ne, maimakon ba da kulawa ga kasashe masu tasowa.

Alal misali, da yawa daga cikin shugabannin kasashen Afirka sun bayyana cewa, matsayin dalar Amurka mai muhimmanci ya hana tattalin arzikin kasashensu ci gaba. Saboda yadda kasar Amurka ke kara kudin ruwan ajiya a kai a kai ya haddasa hauhawar darajar kudin kasar, wanda ke sanya sauran kasashe kashe kudi fiye da kima don shigar da kayayyaki daga ketare, gami da karuwar yawan basusukan da ake binsu. Game da matsalolin da karuwar darajar dalar Amurka ke haddasa wa tattalin arzikin sauran kasashe, na san abokanmu dake Najeriya sun fahimce su sosai.

Sa’an nan a fannin harkar siyasar kasa da kasa, kasar Amurka da kawayenta na yammacin duniya sun sa hannu cikin rikicin dake tsakanin Rasha da Ukraine, inda suke ba da taimako ga wani bangare, gami da tilastawa sauran kasashe bin sahunsu. Sai dai kasashen Afirka suna son ci gaba da hadin gwiwa da kasar Rasha, da neman ganin an kawo karshen yakin da ake yi cikin sauri, kuma ta hanyar lumana, bisa la’akari da moriya kansu.

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

A sa’i daya, kasashen Afirka da kasashe masu tasowa na sauran yankuna suna son ganin gyare-gyare kan tsare-tsaren bankin duniya, da hukumar ba da lamuni ta duniya, da kasashen yamma suka kafa, don magance samar da karin tallafi ga kasashe masu sukuni, maimakon kula da kasashe marasa karfi. Wadannan abubuwan da na ambata suna cikin cece-kuce da ake samu tsakanin kasashe masu tasowa, da kasashen yamma, sakamakon bambancin moriyar su.

Saboda haka, yadda tsarin BRICS yake habaka, da yadda yake sa kaimi ga yin kwaskwarima kan tsarin hada-hadar kudi na duniya, sun yi daidai da bukatun dimbin kasashe masu tasowa. Inda a ganinsu, ci gaban da tsarin BRICS ya samu ya nuna yadda kasashe masu tasowa ke samun karin ikon fada a ji a duniya, da karin damammaki na tabbatar da moriyarsu. Batun nan ya yi kama da maganar da shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya fada a wajen taron kolin BRICS na wannan karo, inda ya ce, ya kamata kasashen BRICS su haifar da sauyin yanayi ga tsarin kula da duniya, don neman tabbatar da adalci da kima, da wani yanayi na tabbas, da karko, gami da ci gaba.

Idan karin kasashe masu tasowa sun karfafa hadin gwiwarsu ta hanyar tsarin BRICS, to, za su samu isashen karfin yin garambawul kan tsare-tsaren duniya. Saboda ko kasashe mambobi guda 5 da suke cikin tsarin a halin yanzu, wato Brazil, da Rasha, da Indiya, da Sin, da Afirka ta Kudu, sun riga sun dauki kaso 24.3 na tattalin arzikin duniya, da kaso 26.46 na fadin harabar kasashen duniya, gami da kaso 43 na daukacin al’ummar duniya. Yayin da ake sa ran ganin karuwar wadannan adadi a kai a kai a nan gaba. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa
Daga Birnin Sin

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Next Post
Shugaba Xi Jinping Da Takwaransa Na Afirka Ta Kudu Sun Jagoranci Taron Tattaunawa A Tsakanin Shugabannin Sin Da Afirka

Shugaba Xi Jinping Da Takwaransa Na Afirka Ta Kudu Sun Jagoranci Taron Tattaunawa A Tsakanin Shugabannin Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version