• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin Tantance Ayyukan Likitanci A Sararin Samaniya Zai Ingiza Nasarar Binciken Samaniya

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Tsarin Tantance Ayyukan Likitanci A Sararin Samaniya Zai Ingiza Nasarar Binciken Samaniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manazarta ayyukan sama jannati sun bayyana cewa, tsarin tantance ayyukan likitanci na sararin samaniya, zai ingiza nasarar binciken samaniya yadda ya kamata.

 

Yayin taron dandali na biyu game da binciken tsarin ayyukan likitanci na sararin samaniya na kasar Sin da aka bude a Asabar din nan a birnin Hangzhou, na lardin Zhejiang dake gabashin kasar Sin, mahalarta taron sun ce cibiyar binciken samaniya ta Sin ta cimma nasarori a fannin tsarin ayyukan likitanci na sararin samaniya, wanda hakan zai ingiza nasarar shirin sauka a duniyar wata, da sauran ayyuka masu nasaba da aikin sama jannati.

  • Xi Ya Jaddada Samar Da Karin Kwararrun Jami’ai Ga Xinjiang
  • Fasahar Sin Ta Kara Habaka Sha’anin Zirga-zirgar Ababen Hawa Mara Gurbata Muhalli A Afrika

Yayin taron na yini biyu, kwararru da masana za su yi musaya kan nazari, da ayyukan ci gaba da aka lalubo a fannin tsarin ayyukan likitanci na sararin samaniya, kana za a tattauna kan muhimman batutuwa, kamar yiwuwar dan Adam ya rayu a yankunan samaniya masu nisa yayin ayyukan sama jannati.

 

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Da yake tsokaci game da hakan yayin bude taron, mataimakin shugaban tsare tsaren ayyukan sama jannati na kasar Sin, kana dan sama jannati na farko a kasar Sin Yang Liwei, ya ce tallafin samar da kwarewa a fannonin ayyukan likitanci na sararin samaniya, muhimmin bangare ne na wanzar da ci gaban ayyukan bunkasa bincike, a cibiyar binciken samaniya ta kasar Sin, da tsarin aiwatar da shirin binciken duniyar wata na ‘yan sama jannati, wanda dukkaninsu suka haifar da sabbin damammaki a fannin bunkasa tsarin ayyukan likitanci na sararin samaniya.

 

Bugu da kari, tsarin ayyukan likitanci na sararin samaniya na taka muhimmiyar rawa wajen cimma nasarar kiwon lafiyar al’umma. Tare da samar da tallafi, da dandalin gudanar da bincike kan sassan kula da lafiyar zuciya, da sassan tsoka da kashin ‘yan sama jannati, da batun tsufan jikin dan adam, da samar da kariya ga magunguna, da tantance ingancin su. (Mai fassara: Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gudanar Da Bikin Da Ya Shafi Makamashi Na Nan Gaba A Birnin New York

Next Post

Sin Ta Cimma Nasarar Kera Maganadisu Mafi Karfi A Duniya

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

5 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

6 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

7 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

8 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

10 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

1 day ago
Next Post
Sin Ta Cimma Nasarar Kera Maganadisu Mafi Karfi A Duniya

Sin Ta Cimma Nasarar Kera Maganadisu Mafi Karfi A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.