• English
  • Business News
Thursday, August 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin Tinubu Kan Raya Albarkatun Kiwo Da Samar Da Abinci Yana Haifar Da Ɗa Mai Ido – Minista

by Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Tsarin Tinubu Kan Raya Albarkatun Kiwo Da Samar Da Abinci Yana Haifar Da Ɗa Mai Ido – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jinjina wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu kan kafa Ma’aikatar Raya Albarkatun Kiwon Dabbobi, ya ce hakan wani muhimmin tsari ne na amfani da damar da ke cikin ɓangaren kiwo da kuma inganta sarrafa kayayyakin da ake samarwa.

 

Idris ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a lokacin da yake jawabi a Taron Shekara-shekara na Hukumar Gidajen Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN) da aka gudanar a Abuja, mai taken “Samar da Abinci a Nijeriya: Ina Mafita?”

  • Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Legas Za Ta Kara Samar Da Kwararru – Kwamishina
  • Mutum 10 Sun Mutu A Turmutsutsin Rabon Shinkafa A Abuja

Ya ce: “Ba a jima ba da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu (GCFR), ya ɗauki wani gagarumin mataki na kafa Ma’aikatar Raya Albarkatun Kiwon Dabbobi. Wannan tsari mai muhimmanci ya nuna yadda gwamnatin ta fahimci irin damar da ke cikin harkar kiwon dabbobi, wanda ake kira tushen da ba a yi amfani da shi ba.”

 

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

Ministan ya jaddada cewa tabbatar da wadatar abinci yana da matuƙar muhimmanci ga tsaron ƙasa, zaman lafiya, da cin gashin kai.

 

Wannan ne ya sa Shugaba Tinubu ya sake fasalin sunan Ma’aikatar Noma da Raya Yankunan Karkara zuwa Ma’aikatar Noma da Samar da Abinci.

 

Ya ce: “Nijeriya, wadda Allah ya albarkace ta da ƙasa mai yalwa, yanayi mai kyau, da matasa da ke cike da kuzari, tana da damar zama jagorar noma a duniya. Amma har yanzu muna fama da ƙalubale wajen samar da abinci mai arha kuma wadatacce.

 

“Wannan ƙalubale ne da ya sa Shugaban Ƙasa ya mai da hankali sosai ga wannan muhimmin ɓangare, wanda shi ne babbar hanyar samar da ayyukan yi a ƙasar nan.”

 

Idris ya bayyana cewa gwamnatin ta ɗauki matakai masu muhimmanci, ciki har da ayyana dokar ta-ɓaci kan samar da abinci, ƙaddamar da shirin samar da abinci mai ɗorewa, da kuma yaƙi da masu ɓoye kaya da masu fasa-ƙwauri, domin tabbatar da samun kayan abinci cikin sauƙi da arha.

 

“Babu abin da ba za a iya cimmawa ba wajen samar da abinci a Nijeriya, musamman idan muka haɗa kai; za mu iya canza ƙasar mu zuwa ƙasar da take da yalwar abinci, inda babu wani ɗan Nijeriya da zai kwanta da yunwa.

 

“Na tabbata cewa babban baƙo mai gabatar da jawabi da sauran ƙwararru za su yi cikakken bayani kan ƙalubalen da harkar noma ke fuskanta tare da bayar da hanyoyin magance su,” inji shi.

 

Ministan ya kuma yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su taka muhimmiyar rawa wajen inganta samar da abinci ta hanyar ilimantar da manoma kan dabarun zamani, canjin yanayi, da kuma tallafin da gwamnati ke bayarwa domin ƙara yawan amfanin gona.

 

Idris ya yaba wa FRCN bisa farfaɗo da wannan Taron Shekara-shekara ɗin, inda ya yaba da ƙudirin ta na bunƙasa cigaban ƙasa ta hanyar shirye-shirye da kuma tsare-tsare masu tasiri.

 

Taron ya samu halartar manyan baƙi kamar Ministan Raya Albarkatun Kiwon Dabbobi, Alhaji Idi Muktar; Ƙaramin Ministan Noma da Tabbatar da Wadatar Abinci, Sanata Aliyu Sabi Abdullahi; Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli; da Sarkin Wase a Jihar Filato, Alhaji Muhammadu Sambo Haruna.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dangote Ya Yabi Tinubu Kan Tasirin Yarjejeniyar Musanyar Fetur da Naira

Next Post

An Bude Sabon Babi A Yankin Macao Wajen Aiwatar Da Manufar Kasa Daya Mai Tsarin Mulki Biyu A Cikin Shekaru 25

Related

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

45 minutes ago
Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano
Labarai

Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

3 hours ago
Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II
Manyan Labarai

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

4 hours ago
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025
Labarai

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

12 hours ago
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna
Labarai

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

13 hours ago
Tinubu
Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

14 hours ago
Next Post
An Bude Sabon Babi A Yankin Macao Wajen Aiwatar Da Manufar Kasa Daya Mai Tsarin Mulki Biyu A Cikin Shekaru 25

An Bude Sabon Babi A Yankin Macao Wajen Aiwatar Da Manufar Kasa Daya Mai Tsarin Mulki Biyu A Cikin Shekaru 25

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

August 7, 2025
An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

An Bude Bikin Fina-Finan Kasar Sin A Zimbabwe

August 7, 2025
Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

Jama’a Suke Tona Asirin Gurɓatattun Jami’anmu – Kwamishinan ‘Yansandan Kano

August 7, 2025
Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

August 7, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan

August 6, 2025
Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

Yanzu-yanzu: WAEC Ta Rufe Shafin Duba Jarabawar WASSCE 2025

August 6, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

Hukumar Kwastam Ta Kama Tankar Mai Dauke Da Buhunan Shinkafa A Kaduna

August 6, 2025
Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

Yadda Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Fara Yada Shirye-shiryenta Na Rediyo Da Sinanci

August 6, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Bayar Da Kiwon Lafiya Kyauta Ga ‘Yan Fansho Masu Karamin Karfi 

August 6, 2025
Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

Za A Watsa Shirin Talabijin Don Bayyana Tunanin Al’adu Na Xi Jinping

August 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.