• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsarin Tinubu Kan Raya Albarkatun Kiwo Da Samar Da Abinci Yana Haifar Da Ɗa Mai Ido – Minista

by Sulaiman
9 months ago
in Labarai
0
Tsarin Tinubu Kan Raya Albarkatun Kiwo Da Samar Da Abinci Yana Haifar Da Ɗa Mai Ido – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jinjina wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu kan kafa Ma’aikatar Raya Albarkatun Kiwon Dabbobi, ya ce hakan wani muhimmin tsari ne na amfani da damar da ke cikin ɓangaren kiwo da kuma inganta sarrafa kayayyakin da ake samarwa.

 

Idris ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a lokacin da yake jawabi a Taron Shekara-shekara na Hukumar Gidajen Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN) da aka gudanar a Abuja, mai taken “Samar da Abinci a Nijeriya: Ina Mafita?”

  • Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Legas Za Ta Kara Samar Da Kwararru – Kwamishina
  • Mutum 10 Sun Mutu A Turmutsutsin Rabon Shinkafa A Abuja

Ya ce: “Ba a jima ba da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu (GCFR), ya ɗauki wani gagarumin mataki na kafa Ma’aikatar Raya Albarkatun Kiwon Dabbobi. Wannan tsari mai muhimmanci ya nuna yadda gwamnatin ta fahimci irin damar da ke cikin harkar kiwon dabbobi, wanda ake kira tushen da ba a yi amfani da shi ba.”

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Ministan ya jaddada cewa tabbatar da wadatar abinci yana da matuƙar muhimmanci ga tsaron ƙasa, zaman lafiya, da cin gashin kai.

 

Wannan ne ya sa Shugaba Tinubu ya sake fasalin sunan Ma’aikatar Noma da Raya Yankunan Karkara zuwa Ma’aikatar Noma da Samar da Abinci.

 

Ya ce: “Nijeriya, wadda Allah ya albarkace ta da ƙasa mai yalwa, yanayi mai kyau, da matasa da ke cike da kuzari, tana da damar zama jagorar noma a duniya. Amma har yanzu muna fama da ƙalubale wajen samar da abinci mai arha kuma wadatacce.

 

“Wannan ƙalubale ne da ya sa Shugaban Ƙasa ya mai da hankali sosai ga wannan muhimmin ɓangare, wanda shi ne babbar hanyar samar da ayyukan yi a ƙasar nan.”

 

Idris ya bayyana cewa gwamnatin ta ɗauki matakai masu muhimmanci, ciki har da ayyana dokar ta-ɓaci kan samar da abinci, ƙaddamar da shirin samar da abinci mai ɗorewa, da kuma yaƙi da masu ɓoye kaya da masu fasa-ƙwauri, domin tabbatar da samun kayan abinci cikin sauƙi da arha.

 

“Babu abin da ba za a iya cimmawa ba wajen samar da abinci a Nijeriya, musamman idan muka haɗa kai; za mu iya canza ƙasar mu zuwa ƙasar da take da yalwar abinci, inda babu wani ɗan Nijeriya da zai kwanta da yunwa.

 

“Na tabbata cewa babban baƙo mai gabatar da jawabi da sauran ƙwararru za su yi cikakken bayani kan ƙalubalen da harkar noma ke fuskanta tare da bayar da hanyoyin magance su,” inji shi.

 

Ministan ya kuma yi kira ga kafafen yaɗa labarai da su taka muhimmiyar rawa wajen inganta samar da abinci ta hanyar ilimantar da manoma kan dabarun zamani, canjin yanayi, da kuma tallafin da gwamnati ke bayarwa domin ƙara yawan amfanin gona.

 

Idris ya yaba wa FRCN bisa farfaɗo da wannan Taron Shekara-shekara ɗin, inda ya yaba da ƙudirin ta na bunƙasa cigaban ƙasa ta hanyar shirye-shirye da kuma tsare-tsare masu tasiri.

 

Taron ya samu halartar manyan baƙi kamar Ministan Raya Albarkatun Kiwon Dabbobi, Alhaji Idi Muktar; Ƙaramin Ministan Noma da Tabbatar da Wadatar Abinci, Sanata Aliyu Sabi Abdullahi; Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmed Nuhu Bamalli; da Sarkin Wase a Jihar Filato, Alhaji Muhammadu Sambo Haruna.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dangote Ya Yabi Tinubu Kan Tasirin Yarjejeniyar Musanyar Fetur da Naira

Next Post

An Bude Sabon Babi A Yankin Macao Wajen Aiwatar Da Manufar Kasa Daya Mai Tsarin Mulki Biyu A Cikin Shekaru 25

Related

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai
Labarai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

24 minutes ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

2 hours ago
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Manyan Labarai

Gwamna Uba Sani Ya Buƙaci Al’ummar Jihar Kaduna Da Su Yi Rijistar Katin Zaɓe 

3 hours ago
DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu
Manyan Labarai

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

5 hours ago
PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu
Manyan Labarai

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

6 hours ago
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME
Ilimi

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

7 hours ago
Next Post
An Bude Sabon Babi A Yankin Macao Wajen Aiwatar Da Manufar Kasa Daya Mai Tsarin Mulki Biyu A Cikin Shekaru 25

An Bude Sabon Babi A Yankin Macao Wajen Aiwatar Da Manufar Kasa Daya Mai Tsarin Mulki Biyu A Cikin Shekaru 25

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

September 8, 2025
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

September 8, 2025
Tinubu

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024

September 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

September 8, 2025
Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

September 8, 2025
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Buƙaci Al’ummar Jihar Kaduna Da Su Yi Rijistar Katin Zaɓe 

September 8, 2025
Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

September 8, 2025
DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

September 8, 2025
PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

September 8, 2025
Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

Kwamitin JAMB Ya Bankaɗo Magudin Jarabawa A 2025 UTME

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.