• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Gwamnatin Tinubu Ta Kashe Naira Tiriliyan 3.2 A Shekara Daya

by Abubakar Abba and Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Tsaro

vector illustration of Nigeria flag and map

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A cikin zango na uku na shekarar 2023 a karkashin gwamantin Shugaban kasa Bola Tinubu, ma’aikatar tsaro ta karbi naira biliyan 412, ma’aikatar kula da harkokin ‘yansanda ta karbi naira biliyan 150, ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara a fannin tsaro, ya karbi naira biliyan 31, inda ma’aikatar kula da harkokin cikin gida ta samu naira biliyan 64, jimlar naira tiriliyan 3.2 aka zuba a fannin tsaron kasar a cikin shekara daya.

A bisa wani bincike da kafar Sahara Reporters ta yi wanda Punch ta wallafa, a 2023, jimlar naira biliyan 657, aka bai wa sashen tsaro a zango na uku.

  • Huawei Ya Kaddamar Da Horo Game Da Tsaron Yanar Gizo Ga Jami’an Zimbabwe
  • Kaico: Wata Mata Ta Bankawa Kanta Wuta A Jigawa

Kazalika, a zango na hudu ma’aikatar tsaro ta karbi naira biliyan 487, ma’aiktar kula da harkokin ‘yansanda ta karbi naira biliyan 282, ma’aikatar kula da harkokin cikin gida ta karbi naira biliyan 119, inda ofishin ma’aikatar tsaro ta karbi naira biliyan 113.

Jimilar naira tiriliyan daya aka bai wa hukumomin tsaro da kuma ma’aikatun tsaro a zango na hudu na 2023.

Hakan ya nuna cewa daga zango na uku zuwa na hudu na 2023, jimlar naira tiriliyan 1.657 aka bai wa hukumomin tsaro da ma’aikatu.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

A bisa nazarin da aka yi na biyan kudaden da gwamnatin tarayya ta yi, ya nuna cewa daga watan Janairu zuwa Yuni na tsakiyar shekarar 2024, jimilar naira 1.032 tiriliyan aka bai wa ma’aiktar tsaro.

Akwai kuma karin wasu naira biliyan 424 da gwamnatin ta bai wa ma’aikatar kula da harkokin ‘yansanda, inda kuma aka bai wa ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara naira biliyan 223. Wannan ya kai jimlar naira triliyan 1.6, da aka bayar a cikin watannin shida.

Gaba dayan wadannan kudaden da gwamnatin ta bayar a cikin watannin shida, rundunar soji kasa ta samu naira biliyan 426, inda rundunar sojin ruwa aka ba ta naira biliyan 140, sai kuma rundunar sojin sama an ba ta naira biliyan 121. Sannan hukumar leken asiri an ba ta naira biliyan 13.7.

A zango na uku 2023 da kuma a zango na biyu na 2024, gwamnatin ta bai wa ma’aikataun tsaro da hukumomin tsaro naira tiriliyan 3.2.

Baya ga gwamnatin tarayya da take bayar da kudade, haka suma gwamnatocin jihohi na bayar da kudade don a magance kalubalen na rashin tsaro a jihohinsu.

Duba da ci gaba da samun karuwar kalubalen rashin tsaron a kasar nan ne ya sanya jihohin da ke a kudu maso yammacin kasar nan, suka fara kirkiro da nasu jami’an tsaron na sa-kai da suka yi wa lakabi da “Amotekun”.

A cikin kasar nan, fannin tsaro na daga cikin jeren ayyukan da gwamnatin tarayya ke kula da shi.

Wasu na cewa, kwalliya na biyan kudin sabulu biyo bayan kirkiro da jami’an tsaron na sa-kai, sai dai, duk da haka akwai sauran rina a kaba na kalubalen rashin tsaron a yankin na kudu maso yamma.

Wasu mata a Jihar Ondo, sun gudanar da zanga-zangar lumana a tsirara, saboda satar manoma da ake yi a gonakansu.

Gwamnatin Ondo ta kashe naira biliyan 3.6 a kan jami’an tsaron sa-kai na Amotekun a cikin watanni 27, amma duk da haka, al’ummomin yankin na ci gaba da zama a cikin fargaba.

Gwamnatin Jihar Osun ta yi kasafin naira miliyan 100 a kan jami’an tsaron sa-kai na Amotekun a 2024, inda ya zuwa yanzu gwamnatin ta kashe naira miliyan 39 a cikin wata shida a 2024.

Jihohi da dama sun zuba makudan kudade a kan jami’an tsaro na sintiri da suka kirkiro da su, inda har wasun su suka kakkafa ma’aikatar tsaro na cikin gida suka kuma jibga dimbin kudade, amma har yanzu lamarin kamar jiya iyau.

Misalil, a Jihar Katsina da ke a arewa maso yamma, gwamnatin jihar ta yi kasafin kudi na naira biliyan 3.4 a cikin harkokin tsaro na cikin gidanta a 2024, inda ya zuwa yanzu, ta kashe naira miliyan 514 a cikin watanni shida.

Haka takwararta ta Jihar Kaduna da ke a yankin na arewa maso yamma, ta zuba naira biliyan 15.4 ga ma’aikatar kula da harkokin tsaronta na cikin gida a 2024.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matawalle Ya Ba Da Umarnin Kamo WaÉ—anda Suka Kashe Sarkin Gobir

Next Post

Kisan Gillar Basaraken Daular Gobir A Hannun Masu Garkuwa Ta Girgiza Al’umma

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

4 hours ago
Tsaro
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

4 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

5 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

8 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

11 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

12 hours ago
Next Post
ÆŠan Sarkin Gobir Da Aka Kashe Ya KuÉ“uta Daga Hannun ‘Yan Bindiga

Kisan Gillar Basaraken Daular Gobir A Hannun Masu Garkuwa Ta Girgiza Al’umma

LABARAI MASU NASABA

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Tsaro

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.