ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Gwamnatin Tinubu Ta Kashe Naira Tiriliyan 3.2 A Shekara Daya

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 years ago
vector illustration of Nigeria flag and map

vector illustration of Nigeria flag and map

A cikin zango na uku na shekarar 2023 a karkashin gwamantin Shugaban kasa Bola Tinubu, ma’aikatar tsaro ta karbi naira biliyan 412, ma’aikatar kula da harkokin ‘yansanda ta karbi naira biliyan 150, ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara a fannin tsaro, ya karbi naira biliyan 31, inda ma’aikatar kula da harkokin cikin gida ta samu naira biliyan 64, jimlar naira tiriliyan 3.2 aka zuba a fannin tsaron kasar a cikin shekara daya.

A bisa wani bincike da kafar Sahara Reporters ta yi wanda Punch ta wallafa, a 2023, jimlar naira biliyan 657, aka bai wa sashen tsaro a zango na uku.

  • Huawei Ya Kaddamar Da Horo Game Da Tsaron Yanar Gizo Ga Jami’an Zimbabwe
  • Kaico: Wata Mata Ta Bankawa Kanta Wuta A Jigawa

Kazalika, a zango na hudu ma’aikatar tsaro ta karbi naira biliyan 487, ma’aiktar kula da harkokin ‘yansanda ta karbi naira biliyan 282, ma’aikatar kula da harkokin cikin gida ta karbi naira biliyan 119, inda ofishin ma’aikatar tsaro ta karbi naira biliyan 113.

ADVERTISEMENT

Jimilar naira tiriliyan daya aka bai wa hukumomin tsaro da kuma ma’aikatun tsaro a zango na hudu na 2023.

Hakan ya nuna cewa daga zango na uku zuwa na hudu na 2023, jimlar naira tiriliyan 1.657 aka bai wa hukumomin tsaro da ma’aikatu.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

A bisa nazarin da aka yi na biyan kudaden da gwamnatin tarayya ta yi, ya nuna cewa daga watan Janairu zuwa Yuni na tsakiyar shekarar 2024, jimilar naira 1.032 tiriliyan aka bai wa ma’aiktar tsaro.

Akwai kuma karin wasu naira biliyan 424 da gwamnatin ta bai wa ma’aikatar kula da harkokin ‘yansanda, inda kuma aka bai wa ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara naira biliyan 223. Wannan ya kai jimlar naira triliyan 1.6, da aka bayar a cikin watannin shida.

Gaba dayan wadannan kudaden da gwamnatin ta bayar a cikin watannin shida, rundunar soji kasa ta samu naira biliyan 426, inda rundunar sojin ruwa aka ba ta naira biliyan 140, sai kuma rundunar sojin sama an ba ta naira biliyan 121. Sannan hukumar leken asiri an ba ta naira biliyan 13.7.

A zango na uku 2023 da kuma a zango na biyu na 2024, gwamnatin ta bai wa ma’aikataun tsaro da hukumomin tsaro naira tiriliyan 3.2.

Baya ga gwamnatin tarayya da take bayar da kudade, haka suma gwamnatocin jihohi na bayar da kudade don a magance kalubalen na rashin tsaro a jihohinsu.

Duba da ci gaba da samun karuwar kalubalen rashin tsaron a kasar nan ne ya sanya jihohin da ke a kudu maso yammacin kasar nan, suka fara kirkiro da nasu jami’an tsaron na sa-kai da suka yi wa lakabi da “Amotekun”.

A cikin kasar nan, fannin tsaro na daga cikin jeren ayyukan da gwamnatin tarayya ke kula da shi.

Wasu na cewa, kwalliya na biyan kudin sabulu biyo bayan kirkiro da jami’an tsaron na sa-kai, sai dai, duk da haka akwai sauran rina a kaba na kalubalen rashin tsaron a yankin na kudu maso yamma.

Wasu mata a Jihar Ondo, sun gudanar da zanga-zangar lumana a tsirara, saboda satar manoma da ake yi a gonakansu.

Gwamnatin Ondo ta kashe naira biliyan 3.6 a kan jami’an tsaron sa-kai na Amotekun a cikin watanni 27, amma duk da haka, al’ummomin yankin na ci gaba da zama a cikin fargaba.

Gwamnatin Jihar Osun ta yi kasafin naira miliyan 100 a kan jami’an tsaron sa-kai na Amotekun a 2024, inda ya zuwa yanzu gwamnatin ta kashe naira miliyan 39 a cikin wata shida a 2024.

Jihohi da dama sun zuba makudan kudade a kan jami’an tsaro na sintiri da suka kirkiro da su, inda har wasun su suka kakkafa ma’aikatar tsaro na cikin gida suka kuma jibga dimbin kudade, amma har yanzu lamarin kamar jiya iyau.

Misalil, a Jihar Katsina da ke a arewa maso yamma, gwamnatin jihar ta yi kasafin kudi na naira biliyan 3.4 a cikin harkokin tsaro na cikin gidanta a 2024, inda ya zuwa yanzu, ta kashe naira miliyan 514 a cikin watanni shida.

Haka takwararta ta Jihar Kaduna da ke a yankin na arewa maso yamma, ta zuba naira biliyan 15.4 ga ma’aikatar kula da harkokin tsaronta na cikin gida a 2024.

Tsaro
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware
Tsaro
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • Sulaiman
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • Sulaiman
    Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba
Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi
Labarai

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Next Post
Ɗan Sarkin Gobir Da Aka Kashe Ya Kuɓuta Daga Hannun ‘Yan Bindiga

Kisan Gillar Basaraken Daular Gobir A Hannun Masu Garkuwa Ta Girgiza Al’umma

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.