• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Matakin Gina Titi Kilomita 108 Cikin Gaggawa

by Sulaiman and Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Matakin Gina Titi Kilomita 108 Cikin Gaggawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da aikin hanyar Magami zuwa Ɗansadau mai tsawon kilomita 108.

 

Gwamnan ya amince da aikin hanyar ne yayin da ya jagoranci taron Majalisar Zartarwa ta Jihar Zamfara a ranar Litinin da ta gabata a gidan gwamnati da ke Gusau.

  • Kiran Tada Hankali A Zanga-zanga: Rundunar ‘Yansanda Ta Cafke Wani Dan TikTok A Filato
  • Kamfanin MTN Ya Rufe Ofishoshinsa A Fadin Nijeriya 

A cikin wata sanarwa da Mai Magana da Yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa, an ɗauki aikin hanyar Magami zuwa Ɗansadau ne a matakin gaggawa domin magance matsalar tsaro da kuma bai wa al’ummar yankin fifiko don jin daɗin rayuwar su.

 

Labarai Masu Nasaba

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Sanarwar ta ƙara da cewa, a tarona majalisar zaryarwar, an tattauna muhimman batutuwa da suka haɗa da yadda ake gudanar da kasafin kuɗi.

 

“Gwamna Dauda Lawal ne ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar Zamfara, wanda ya gudana jiya.

 

“A taron, gwamnan ya amince da sake gina hanyar Magami zuwa Ɗansadau.

 

“Aikin titin mai tsawon kilomita 108, kamar yadda aka bayyana a cikin kasafin kuɗin shekarar 2024, ma’aikatar ayyuka da samar da ababen more rayuwa ta samu amincewar gwamnan na fara aikin, tare da bin tsarin da ya dace na bayar da kwangila, da ba da izini da kuma takardar shaidar aiki ba tare da wata matsala ba daga Hukumar Sayen Kayayyakin Gwamnatin (BPP).

 

“Gwamnan ya amince da bayar da kwangilar ga kamfanin ‘Dantata and Sawoe Construction Co. Ltd’, a matsayin kwangilar da za a yi ta cikin watanni 18 a kan kuɗi Naira 81,189,223,505.73.”

 

Manyan abubuwan da aikin ya ƙunsa sun haɗa da; tsaftace dukkan wuraren da aikin zai shafa, cire kayan da ba su dace ba da maye gurbinsu, tare da ingantattun kayan da aka yarda da su, da samar da magudanan ruwa ingantattu, da sanya gadoji a wuraren da suka dace.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Kawo Matasa Zuwa Yankin Xizang Na Kasar Sin?

Next Post

Me Ya Sa Sin Da Italiya Suke Dora Muhimmanci Kan “Ruhin Hanyar Siliki”?

Related

Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

4 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

5 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

6 hours ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

7 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

9 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

10 hours ago
Next Post
Me Ya Sa Sin Da Italiya Suke Dora Muhimmanci Kan “Ruhin Hanyar Siliki”?

Me Ya Sa Sin Da Italiya Suke Dora Muhimmanci Kan “Ruhin Hanyar Siliki”?

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.