• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Wainar Da Aka Toya A Taron Gwamnoni Da Sarakunan Arewa A Abuja

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
Tsaro: Wainar Da Aka Toya A Taron Gwamnoni Da Sarakunan Arewa A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon yawaitar rashin tsaro a Nijeriya musamman a yankin arewa ta sa gwamnoni da sarakunan gargajiya na yankin sun goyi bayan kafa ‘yansandan jihohi.

A ranar Talata da ta gabata ce, kungiyar gwamnonin arewa (NGF) suka gana da majalisar sarakunan gargajiya na arewa a Abuja, wanda sakamakon ganawar suka bullo da kudurin kafa ‘yansandan jihohi domin dakile matsalar tsaro a yankin da ma Nijeriya gaba daya.

  • Kotu Ta Dage Karar Da Gwamnatin Tarayya Ta Kai ASUU

LEADERSHIP ta ruwaito cewa majalisar kasa ta dade tana watsi da kiraye-kirayen kafa ‘yansandan jihohi lokacin gyaran tsarin mulki, bisa fargabar gwamnonin na iya amdani da su ba bisa ka’ida ba.
Daga cikin matsaloli da aka tattauna a karshen wannan ganawa da ta gudana a otel din Transcorp Hilton da ke Abuja, ‘yan siyasan arewa da sarakunan gargajiya sun sake bibiyar matsalar tsaro a yankin arewa da sauran matsaloli da suka hana yankin ci gaba tare da kawo mafita da kuma goyon bayan yi wa tsarin mulki kuskwarima ta yadda za a samu damar kafa ‘yansandan jihohi.

Shugaban kungiyar gwamnonin arewa kuma gwamnan Jihar Filato, Rt. Hon Simon Lalong shi ne ya karanta manyan batutuwan taron, inda ya bayyana cewa samar da ‘yansandar jihohi zai magance matsalolin tsaro da suka addabi yankin.
A bangaren sakarunan gargajiya kuwa, Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III shi ne ya jaroranci sarakunan, wanda suka hada har da Shehun Borno, Sarkin Kano, Zazzau, Fika, Lafiya, Anka, Gumi, Attah Igala, Ochi Doma, Aku Uka na Wukari da dai sauransu.

Shugabannin dai sun bayyana cewa sun tattauna ne kan al’amuran da suka shafi tsaro da inganta rayuwar al’umma da noma da kasuwanci da zuba jari da nauyin da suka rataya a kan sarakunan gargajiya wajen samar da zaman lafiya da tsaro a yankin arewa.

Labarai Masu Nasaba

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

Tattaunawar ta samu halartar wakilan kungoyoyin fararen hula da suka hada da Kungiyar Mata ta NFWP’ da ta bunkasa ilimin ‘ya`ya mata ta AGILE’, wanda dukkan su bankin duniya ne ya kafa su.
A halin da ake cikin kuma, Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa gwamnatinsa ta yi matukar kokari wajen samar da tsaro da ababen more rayuwa.

Shugaban kasan ya bayyana hakan ne lokacin da yake yi wa masu ruwa da tsaki jawabi a fadar gwamnatin Jihar Imo da ke Owerri bayan da ya kaddamar da babban hanyar Owerri zuwa Orlu da na Owerri zuwa Okigwe da sake gyaran ginin majalisar dokokin jihar da gwamna Hope Uzodimma ya yi.
Ya ce duk da karancin kudade da gwamnatinsa ta fuskanta ta samu nasarori masu dinbin yawa.
“Gwamnatina ta samu nasarar magance matsalolin ababen more rayuwa da na tsaro a Nijeriya idan aka kwatanta da shekarun da ke tsakanin 1999 har zuwa 2015 lokacin da muka karbi mulki,” in ji shi.

Shugaban Buhari ya yaba wa gwamnatinsa bisa kokarin magance matsalolin Boko Haram a yankin arewa maso gabas da inganta ababen more rayuwa wanda gwamnatinsa ta gada tun a lokacin zamanin mulkin PDP.
Buhari ya ce gwamnatin tarayya za ta ci gaba da goyon bayan gwamnatin Jihar Imo da na sauran jihohi domin samar da kyakkyawan dimokoradiyya wanda mutane za su yi alfahari da akidar jam’iyyarsu.

A nasa bangaren kuwa, shugaban kugiyar Ohanaeze Ndigbo, Farfesa George Obiozor ya bayyana cewa rashin tsaro da karancin ababen more rayuwa su ne babban matsaloli guda biyu da suke addabar yankin kudu maso gabashin Nijeriya. Ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yi kokarin magance wadannan matsaloli guda biyu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bukatar Kauce Wa Tasirin Kudi A Zabukan 2023 (Ra’ayinmu)

Next Post

NDLEA Ta Cafke Mutum 761 Bisa Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kaduna

Related

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

11 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

12 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

13 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

14 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

16 hours ago
Next Post
NDLEA Ta Kwace Maganin Cutar Hauka Mai Nauyin Kilo 150 A Gombe

NDLEA Ta Cafke Mutum 761 Bisa Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

Ɗan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.