• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Wainar Da Aka Toya A Taron Gwamnoni Da Sarakunan Arewa A Abuja

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
Tsaro: Wainar Da Aka Toya A Taron Gwamnoni Da Sarakunan Arewa A Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon yawaitar rashin tsaro a Nijeriya musamman a yankin arewa ta sa gwamnoni da sarakunan gargajiya na yankin sun goyi bayan kafa ‘yansandan jihohi.

A ranar Talata da ta gabata ce, kungiyar gwamnonin arewa (NGF) suka gana da majalisar sarakunan gargajiya na arewa a Abuja, wanda sakamakon ganawar suka bullo da kudurin kafa ‘yansandan jihohi domin dakile matsalar tsaro a yankin da ma Nijeriya gaba daya.

  • Kotu Ta Dage Karar Da Gwamnatin Tarayya Ta Kai ASUU

LEADERSHIP ta ruwaito cewa majalisar kasa ta dade tana watsi da kiraye-kirayen kafa ‘yansandan jihohi lokacin gyaran tsarin mulki, bisa fargabar gwamnonin na iya amdani da su ba bisa ka’ida ba.
Daga cikin matsaloli da aka tattauna a karshen wannan ganawa da ta gudana a otel din Transcorp Hilton da ke Abuja, ‘yan siyasan arewa da sarakunan gargajiya sun sake bibiyar matsalar tsaro a yankin arewa da sauran matsaloli da suka hana yankin ci gaba tare da kawo mafita da kuma goyon bayan yi wa tsarin mulki kuskwarima ta yadda za a samu damar kafa ‘yansandan jihohi.

Shugaban kungiyar gwamnonin arewa kuma gwamnan Jihar Filato, Rt. Hon Simon Lalong shi ne ya karanta manyan batutuwan taron, inda ya bayyana cewa samar da ‘yansandar jihohi zai magance matsalolin tsaro da suka addabi yankin.
A bangaren sakarunan gargajiya kuwa, Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III shi ne ya jaroranci sarakunan, wanda suka hada har da Shehun Borno, Sarkin Kano, Zazzau, Fika, Lafiya, Anka, Gumi, Attah Igala, Ochi Doma, Aku Uka na Wukari da dai sauransu.

Shugabannin dai sun bayyana cewa sun tattauna ne kan al’amuran da suka shafi tsaro da inganta rayuwar al’umma da noma da kasuwanci da zuba jari da nauyin da suka rataya a kan sarakunan gargajiya wajen samar da zaman lafiya da tsaro a yankin arewa.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

Tattaunawar ta samu halartar wakilan kungoyoyin fararen hula da suka hada da Kungiyar Mata ta NFWP’ da ta bunkasa ilimin ‘ya`ya mata ta AGILE’, wanda dukkan su bankin duniya ne ya kafa su.
A halin da ake cikin kuma, Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa gwamnatinsa ta yi matukar kokari wajen samar da tsaro da ababen more rayuwa.

Shugaban kasan ya bayyana hakan ne lokacin da yake yi wa masu ruwa da tsaki jawabi a fadar gwamnatin Jihar Imo da ke Owerri bayan da ya kaddamar da babban hanyar Owerri zuwa Orlu da na Owerri zuwa Okigwe da sake gyaran ginin majalisar dokokin jihar da gwamna Hope Uzodimma ya yi.
Ya ce duk da karancin kudade da gwamnatinsa ta fuskanta ta samu nasarori masu dinbin yawa.
“Gwamnatina ta samu nasarar magance matsalolin ababen more rayuwa da na tsaro a Nijeriya idan aka kwatanta da shekarun da ke tsakanin 1999 har zuwa 2015 lokacin da muka karbi mulki,” in ji shi.

Shugaban Buhari ya yaba wa gwamnatinsa bisa kokarin magance matsalolin Boko Haram a yankin arewa maso gabas da inganta ababen more rayuwa wanda gwamnatinsa ta gada tun a lokacin zamanin mulkin PDP.
Buhari ya ce gwamnatin tarayya za ta ci gaba da goyon bayan gwamnatin Jihar Imo da na sauran jihohi domin samar da kyakkyawan dimokoradiyya wanda mutane za su yi alfahari da akidar jam’iyyarsu.

A nasa bangaren kuwa, shugaban kugiyar Ohanaeze Ndigbo, Farfesa George Obiozor ya bayyana cewa rashin tsaro da karancin ababen more rayuwa su ne babban matsaloli guda biyu da suke addabar yankin kudu maso gabashin Nijeriya. Ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yi kokarin magance wadannan matsaloli guda biyu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bukatar Kauce Wa Tasirin Kudi A Zabukan 2023 (Ra’ayinmu)

Next Post

NDLEA Ta Cafke Mutum 761 Bisa Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kaduna

Related

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana
Labarai

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

2 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

3 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

11 hours ago
Tinubu
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

12 hours ago
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa
Labarai

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

13 hours ago
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
Labarai

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

14 hours ago
Next Post
NDLEA Ta Kwace Maganin Cutar Hauka Mai Nauyin Kilo 150 A Gombe

NDLEA Ta Cafke Mutum 761 Bisa Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.