ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Wainar Da Aka Toya A Taron Gwamnoni Da Sarakunan Arewa A Abuja

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Abuja

Sakamakon yawaitar rashin tsaro a Nijeriya musamman a yankin arewa ta sa gwamnoni da sarakunan gargajiya na yankin sun goyi bayan kafa ‘yansandan jihohi.

A ranar Talata da ta gabata ce, kungiyar gwamnonin arewa (NGF) suka gana da majalisar sarakunan gargajiya na arewa a Abuja, wanda sakamakon ganawar suka bullo da kudurin kafa ‘yansandan jihohi domin dakile matsalar tsaro a yankin da ma Nijeriya gaba daya.

  • Kotu Ta Dage Karar Da Gwamnatin Tarayya Ta Kai ASUU

LEADERSHIP ta ruwaito cewa majalisar kasa ta dade tana watsi da kiraye-kirayen kafa ‘yansandan jihohi lokacin gyaran tsarin mulki, bisa fargabar gwamnonin na iya amdani da su ba bisa ka’ida ba.
Daga cikin matsaloli da aka tattauna a karshen wannan ganawa da ta gudana a otel din Transcorp Hilton da ke Abuja, ‘yan siyasan arewa da sarakunan gargajiya sun sake bibiyar matsalar tsaro a yankin arewa da sauran matsaloli da suka hana yankin ci gaba tare da kawo mafita da kuma goyon bayan yi wa tsarin mulki kuskwarima ta yadda za a samu damar kafa ‘yansandan jihohi.

ADVERTISEMENT

Shugaban kungiyar gwamnonin arewa kuma gwamnan Jihar Filato, Rt. Hon Simon Lalong shi ne ya karanta manyan batutuwan taron, inda ya bayyana cewa samar da ‘yansandar jihohi zai magance matsalolin tsaro da suka addabi yankin.
A bangaren sakarunan gargajiya kuwa, Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III shi ne ya jaroranci sarakunan, wanda suka hada har da Shehun Borno, Sarkin Kano, Zazzau, Fika, Lafiya, Anka, Gumi, Attah Igala, Ochi Doma, Aku Uka na Wukari da dai sauransu.

Shugabannin dai sun bayyana cewa sun tattauna ne kan al’amuran da suka shafi tsaro da inganta rayuwar al’umma da noma da kasuwanci da zuba jari da nauyin da suka rataya a kan sarakunan gargajiya wajen samar da zaman lafiya da tsaro a yankin arewa.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Tattaunawar ta samu halartar wakilan kungoyoyin fararen hula da suka hada da Kungiyar Mata ta NFWP’ da ta bunkasa ilimin ‘ya`ya mata ta AGILE’, wanda dukkan su bankin duniya ne ya kafa su.
A halin da ake cikin kuma, Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa gwamnatinsa ta yi matukar kokari wajen samar da tsaro da ababen more rayuwa.

Shugaban kasan ya bayyana hakan ne lokacin da yake yi wa masu ruwa da tsaki jawabi a fadar gwamnatin Jihar Imo da ke Owerri bayan da ya kaddamar da babban hanyar Owerri zuwa Orlu da na Owerri zuwa Okigwe da sake gyaran ginin majalisar dokokin jihar da gwamna Hope Uzodimma ya yi.
Ya ce duk da karancin kudade da gwamnatinsa ta fuskanta ta samu nasarori masu dinbin yawa.
“Gwamnatina ta samu nasarar magance matsalolin ababen more rayuwa da na tsaro a Nijeriya idan aka kwatanta da shekarun da ke tsakanin 1999 har zuwa 2015 lokacin da muka karbi mulki,” in ji shi.

Shugaban Buhari ya yaba wa gwamnatinsa bisa kokarin magance matsalolin Boko Haram a yankin arewa maso gabas da inganta ababen more rayuwa wanda gwamnatinsa ta gada tun a lokacin zamanin mulkin PDP.
Buhari ya ce gwamnatin tarayya za ta ci gaba da goyon bayan gwamnatin Jihar Imo da na sauran jihohi domin samar da kyakkyawan dimokoradiyya wanda mutane za su yi alfahari da akidar jam’iyyarsu.

A nasa bangaren kuwa, shugaban kugiyar Ohanaeze Ndigbo, Farfesa George Obiozor ya bayyana cewa rashin tsaro da karancin ababen more rayuwa su ne babban matsaloli guda biyu da suke addabar yankin kudu maso gabashin Nijeriya. Ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta yi kokarin magance wadannan matsaloli guda biyu.

Abuja
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
NDLEA Ta Kwace Maganin Cutar Hauka Mai Nauyin Kilo 150 A Gombe

NDLEA Ta Cafke Mutum 761 Bisa Hada-hadar Miyagun Kwayoyi A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.